Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Aikin Shinfida Layin Dogo daga Kano zuwa Katsina Ya Kai Fiye da Kashi 75%
    News

    Aikin Shinfida Layin Dogo daga Kano zuwa Katsina Ya Kai Fiye da Kashi 75%

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 28, 20263 Mins Read
    FB IMG 1787946451581
    FB IMG 1787946451581

    Gwamnatin Tarayya ta sake tabbatar da cewa za a kammala tare da ƙaddamar da sashen Kano–Daura–Katsina na aikin layin dogo na Kano–Maradi, mai tsawon kilomita 284, a watan Disamba 2026.

    Gwamnatin ta bayyana hakan ne bayan wani Ayarin hadin gwiwa daga Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya, Ma’aikatar Kuɗi da kuma masu ba da kuɗin aikin yayin ziyarar duba aikin daga ranar Talata 25 zuwa Alhamis 27 ga Agusta 2026.

    Ayarin sun nuna cewa aikin sashen Kano–Katsina ya kai sama da kashi 75 cikin 100, yayin da aka kuma gudanar da gwajin tafiyar jirgin ƙasa a kan layin da aka kammala, inda jami’an suka yi tafiya daga Kazaure zuwa Katsina.

    Daraktar Sufurin Jiragen Ƙasa ta Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya, Injiniya Habiba Buhari, wadda ta wakilci Babban Sakataren Ma’aikatar, Injiniya Funso Adebiyi, ta ce aikin yana kan hanyar kammaluwa tare da ƙaddamar dashi a watan Disamba 2026.

    Ta ce duk da cewa damina ta ɗan rage saurin aikin, an samu gagarumin ci gaba, musamman ganin cewa an riga an tanadi kayayyakin da ake buƙata domin ci gaba da shimfiɗa layin dogon.

    Sai dai ta bayyana cewa aikin na fuskantar wasu ƙalubale da suka haɗa da matsalolin tsaro, satar kayayyakin gini, matsalolin mallakar filaye da hanyar jirgi ta ratsa a wasu birane, haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba a kan hanyar Kano–Dutse, da kuma raguwar ayyukan gine-gine a lokacin damina.

    Dangane da matsalolin filaye, Injiniya Buhari ta ce gwamnati na tattaunawa da al’ummomin da abin ya shafa domin warware matsalolin tare da tabbatar da cewa ’yan kwangila sun samu damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

    Ta kuma ce ana ci gaba da shirye-shiryen samar da jiragen ƙasan da za su fara aiki domin tabbatar da cewa an samu kayan aikin da ake buƙata kafin lokacin ƙaddamar da aikin.

    Shi ma wakilin masu ba da kuɗin aikin, Siya Biniza, ya bayyana cewa jarin da aka zuba a aikin ya dace, yana mai cewa layin dogo muhimmin ababen more rayuwa ne da zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin Najeriya.

    A nasa ɓangaren, wakilin Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya, Alhaji Muhammadu Kamal, ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta fitar da kashi 15 cikin 100 na kuɗin haɗin gwiwar da ya rataya a kanta.

    Ya ce sauran kashi 85 cikin 100 na kuɗin aikin ana samar da shi ne ta hanyar tsarin tallafin kuɗi na rance.

    Kamfanin da ke aikin, Mota-Engil Nigeria, ya kuma tabbatar da aniyarsa ta kammala sashen Kano–Katsina zuwa Disamba 2026.

    Babban Jami’in Kuɗi na kamfanin, Vladislav Bystrenko, ya ce mataki na farko na aikin, wanda ya haɗa da hanyar Kano–Katsina, zai kammalu a Disamba 2026, yayin da ake sa ran kammala sashen Katsina zuwa Maradi a Jamhuriyar Nijar zuwa ƙarshen shekarar 2027.

    FB IMG 1787946457552
    FB IMG 1787946457552
    be dec kano Katsina line rail ready to
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleNDPC Registers FUE Zaria as Data Controller/Processor of Major Importance
    Next Article NDC COURSE 34 GRADUATION: COAS HONOURED WITH DISTINGUISHED ALUMNUS STAR

    Related Posts

    News

    *NDLEA Honours Muhuyi Magaji as WADA Ambassador, Says No Single Agency Can Win Drug War Alone*

    August 28, 2026
    News

    Support families of missing persons, cleric charges Muslims

    August 28, 2026
    News

    Kaduna Electric Dispute: Millennium City Residents Fear Prolonged Darkness May Worsen Insecurity

    August 28, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026292 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026242 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026223 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026167 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026162 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026155 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.