A ci gaba da rangadin ‘Gani Ya Kori Ji’ domin ganin manyan ayyukan gwamnatin Tarayya a zahiri, ayarin masu aikin jarida sun isa Jihar Nasarawa, inda suka duba wasu muhimman ayyukan raya ƙasa tare da jin ra’ayoyin mazauna yankunan da ayyukan suka shafa.
Ziyarar, wadda ke cikin wani shiri na bai wa masu aikin jarida damar tantance ayyukan gwamnati a zahiri, ta kai ayarin wasu muhimman wurare ƙarƙashin jagorancin jami’an Fadar Shugaban Ƙasa, ciki har da Babban Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, da sauran jami’an yaɗa labarai da suka haɗa da Bayo Onanuga da Dada Olusegun.
Daga cikin wuraren da suka ziyarta akwai katafariyar Sakatariyar Gwamnatin Jihar Nasarawa, wadda ke daga cikin muhimman gine-ginen da ake amfani da su wajen inganta ayyukan gwamnati da samar da ingantaccen yanayi ga ma’aikata da al’umma.
Ayarin sun kuma duba wasu muhimman hanyoyi, ciki har da Hanyar Shabu, wadda ke taka muhimmiyar rawa wajen haɗa al’ummomi da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki. Mazauna yankunan sun bayyana cewa inganta hanyoyin na rage wahalhalun sufuri tare da buɗe ƙofofin kasuwanci, noma da zuba jari.
Wani abin da ya ɗauki hankalin ayarin shi ne yadda ake ƙarfafa matasa ta hanyar koyar da su sana’o’in hannu, musamman walda da sauran ƙwarewar da za su ba su damar dogaro da kansu. Irin waɗannan shirye-shirye na da tasiri sosai wajen rage zaman kashe wando da kuma samar da matasan da za su iya samar wa kansu da iyalansu abin dogaro.
Baya ga hanyoyi da cibiyoyin koyar da sana’o’i, Ayarin sun duba wasu yankunan da ambaliyar ruwa ta taɓa, inda ake aiwatar da ayyukan gyaran kwalbatoci da magudanan ruwa domin rage barazanar ambaliya da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Daga cikin wuraren da aka ziyarta akwai Hanyar Lafiya zuwa Doma da kuma Gadar Kilema a cikin birnin Lafiya. A cewar mazauna yankunan, gyaran irin waɗannan ababen more rayuwa sun taimaka matuka wajen sauƙaƙa zirga-zirga da rage wasu matsalolin da suke fuskanta a kullum.
Mazauna yankunan da ayarin suka ziyarta sun bayyana farin cikinsu kan ayyukan da ake gudanarwa, musamman yadda ake haɗa gina hanyoyi, magudanan ruwa da ƙarfafa sana’o’in matasa da sauran shirye-shiryen bunƙasa rayuwar al’umma.
Wasu daga cikinsu sun bayyana fatan cewa ayyukan za su ci gaba da yaɗuwa zuwa sauran ƙananan hukumomi da al’ummomin jihar, domin ƙarin jama’a su amfana da su.
Abin da aka gani a Nasarawa ya kuma sake bayyana muhimmancin haɗin gwiwar gwamnatin Tarayya da jihohi wajen mayar da manufofin raya ƙasa zuwa ayyukan da jama’a za su iya gani da idonsu. A ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata, masu goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kallon irin waɗannan ayyuka a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin sabunta ababen more rayuwa, ƙarfafa matasa da bunƙasa tattalin arzikin yankunan Arewa.
A jihar Nasarawa, sakon da ayyukan ke isarwa shi ne cewa ci gaba ba wai magana ce kawai ba, ana iya ganinsa a hanyar da aka gyara, matashin da ya samu sana’a, magudanar ruwa da ta kare al’umma daga ambaliya, da kuma sabon aikin da ya buɗe damar kasuwanci.
Sabuwar Nigeria







