Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin tarayya tare da gwamnonin jihohi sun amince da daukar matakan gaggawa domin rage kudin sufuri a fadin ƙasar, musamman ta hanyar amfani da motocin CNG da na lantarki.
Shugaban ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook bayan ganawarsa da Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, inda ya ce gwamnonin sun dauki matakin ne bisa ra’ayinsu domin tabbatar da cewa alfanun sauyin makamashi sun isa ga talakawa.
Ya ce gwamnatin tarayya ta riga ta zuba jari mai yawa wajen sauya motocin daga amfani da man fetur zuwa ruwa man gas na CNG, inda ya bayyana cewa sama da motoci 120,000 aka riga aka mayar da su zuwa amfani da CNG a fadin Najeriya, yayin da ake shirin samar da wasu kayan sauya fiye da 100,000.
A cewar Shugaban, ana kuma ci gaba da fadada cibiyoyin sauya motocin zuwa CNG da kuma samar da kayayyakin da ake bukata domin samun CNG a sassa daban-daban na kasar.
Ya ce ta hannun Midstream and Downstream Gas Infrastructure Fund, gwamnatin tarayya na tallafa wa sama da ayyukan iskar gas 100 a fadin Najeriya, wadanda suka hada da manyan tashoshin CNG 15 da kananan tashoshi 86.
Shugaban ya ce a watan Mayu ya kaddamar da wasu daga cikin wadannan ayyuka a Legas, Abuja da Owerri, ciki har da cibiyar tashoshin CNG guda 15 a Legas da wata cibiya a Abuja da za ta iya yi wa motoci da kekunan hawa 1,000, da manyan motoci da bas 50 hidima a rana.
Ya kuma bayyana cewa ya bayar da umarnin kara samar da wasu tashoshin CNG 500 a fadin kasar, baya ga 500 da asusun ya riga ya bayar da umarnin samarwa a farkon shekarar.
Hakan zai kai yawan tashoshin CNG da ake shirin samarwa zuwa 1,000 a fadin Najeriya.
Shugaban Tinubu ya ce sufuri na cikin gari ne bangaren da ’yan Najeriya suka fi jin tasirin tsadar man fetur, saboda haka jihohi ne ke da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ganin an sauke kudin sufuri.
Ya ce gwamnoni sun amince da kafa kwamitin hadin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da jihohi domin fara aiwatar da matakan rage kudin sufuri nan take.
A cewar Shugaban, motar da ke amfani da CNG na iya kashe kashi 60 zuwa 80 cikin 100 kasa da kudin man fetur wajen tafiya.
Ya ce burin gwamnatin tarayya shi ne daga 1 ga Oktoba, ’yan Najeriya su fara ganin tasirin wannan rangwame ta hanyar saukar kudin sufuri.
“Mun amince cewa idan man fetur ya yi arha, kudin sufuri ma ya kamata ya yi arha,” in ji Shugaban.
Ya ce matakin na bukatar dukkan matakan gwamnati su ci gaba da yin aiki tare domin tabbatar da an samar da sauki ga ’yan Najeriya.
Sabuwar Nigeria.

