Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci jerin sunayen mambobin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugabancin Ƙasa na APC da aka kafa domin tunkarar zaɓen watan Janairun 2027.
A cikin jerin sunayen da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar ranar Asabar, Shugaba Tinubu zai kasance Shugaban kwamitin, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai kasance Mataimakin Sa.
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, shi ma zai kasance Mataimakin Shugaban kwamitin, yayin da tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, aka naɗa Darakta-Janar.
Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, zai kasance Sakataren kwamitin, tare da Sanata Ajibola Bashiru da Hadiza Bala-Usman a matsayin Mataimakin Sakataren da Mataimakiyar Sakatare.
Kwamitin ya kuma naɗa wasu manyan ‘yan siyasa a matsayin masu ba Shugaban Kwamitin shawara, ciki har da Chief Bisi Akande, Chief Segun Osoba, Sanata Rochas Okorocha, Sanata Abdullahi Adamu da Sanata Florence Ita Giwa.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, da Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, za su kasance Mataimakan Darakta-Janar da za su kula da yaƙin neman zaɓe a Kudu da Arewa, tare da Sanata Opeyemi Bamidele da Sanata Barau Jibrin.
Haka kuma, Sanata Adams Oshiomhole zai kasance Mataimakin Darakta-Janar mai kula da gangamin jama’a, yayin da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa zai kasance Mataimakin Darakta-Janar mai kula da harkokin gudanarwa.
An sake naɗa James Abiodun Faleke a matsayin Mataimakin Darakta-Janar mai kula da tsara zaɓe, daidaitawa da sa ido, bayan rawar da ya taka a yaƙin neman zaɓen 2022/2023.
A bangaren yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris Malagi, zai kasance Daraktan Gudanarwa na Yada Labarai da Dabarun Sadarwa, tare da Dele Alake, Bayo Onanuga da Lanre Issa-Onilu.
Tunde Rahman, Sunday Dare, Daniel Bwala da Felix Morka za su kasance Mataimakan Daraktoci masu gudanarwa a wannan sashe.
Abdulaziz AbdulAziz zai yi aiki tare da Temitope Ajayi, Arabinrin Aderonke da Frederick Nwabufor a matsayin Sakatarorin Gudanarwa na bangaren yaɗa labarai.
Segun Dada zai kasance Daraktan Kafofin Sada Zumunta, yayin da Solomon Arowolo zai kasance Sakatare.
Kwamitin ya kuma naɗa Dele Alake a matsayin jagoran masu magana da yawun yaƙin neman zaɓen, tare da Alwan Hassan, Ayobami Oyalowo, Kemi Asekun-Shittu da Adamu Fanda.
Shugaba Tinubu ya buƙaci dukkan mambobin kwamitin da su ƙara himma wajen ganin APC ta samu nasara a zaɓen watan Janairun 2027.
Ya kuma buƙaci shugabannin sassa daban-daban da su haɗa hannu da sauran ‘yan jam’iyyar da ba a saka sunayensu cikin jerin ba, domin su bayar da gudummawarsu wajen ganin an samu nasarar yaƙin neman zaɓen.
Shugaban ya ce gwamnati ta cika alkawuran da ta ɗauka tare da sanya Najeriya a kan turbar ci gaban tattalin arziki, yana mai cewa lokacin yaƙin neman zaɓe ya kamata jam’iyyar ta fito da nasarorin da aka samu domin ƙarfafa gwiwar ‘yan Najeriya.
Ya ce, “Mun cika alkawuran da muka ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe, kuma mun sanya ƙasar nan a kan turbar ci gaban tattalin arziki.”
Sabuwar Nigeria

