Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Shugaba Tinubu ya taya Mai Alfarma Sarkin Musulmi murnar cika shekara 70
    News

    Shugaba Tinubu ya taya Mai Alfarma Sarkin Musulmi murnar cika shekara 70

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 24, 20262 Mins Read
    FB IMG 1787602661138
    FB IMG 1787602661138

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, murnar cika shekara 70 da haihuwa.

    A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Lahadi, Tinubu ya bayyana Sarkin Musulmin a matsayin jagora mai hikima da kishin zaman lafiya.

    Shugaban ya ce shekaru 70 na rayuwar Sarkin Musulmin shaida ne kan rayuwar da ya sadaukar wajen hidima, hikima da jagoranci, musamman tsawon kusan shekaru 20 da ya yi kan karagar mulkin Sarkin Musulmi.

    Ya bayyana cewa Sarkin Musulmin ya kasance murya mai tabbatar da zaman lafiya a lokutan tashin hankali, mai hada kan al’umma da addinai, kuma jagora mai bayar da shawarwari ga Musulmi da sauran al’ummar Najeriya.

    A cewar Tinubu, Sarkin Musulmin ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta ilimi, tattaunawar addinai, ayyukan jin ƙai da zaman lafiya tsakanin al’ummomi, tare da bayar da muhimmiyar gudunmawa wajen kare mutuncin kowane ɗan Najeriya.

    Shugaban ya kuma bayyana cewa yana matuƙar daraja haɗin gwiwar Sarkin Musulmi wajen gina ƙasa, musamman a fannonin tsaro, ci gaban al’umma da kuma inganta rayuwar ’yan Najeriya.

    Tinubu ya yi addu’ar Allah Ya ƙara wa Sarkin Musulmi lafiya, ƙarfi da tsawon rai, tare da kare shi domin iyalansa, masarautar Sokoto da Najeriya baki ɗaya.

    Ya kuma yi fatan wannan shekaru na rayuwar Sarkin Musulmin su kasance mafi alheri da albarka arayuwarsa.

    Sabuwar Nigeria

    congratulates pbat sultan @70
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleAsusun Tallafawa Daliban manyan makarantu,NELFUND ya Yabawa Shugaba Tinubu Kan Dorewar Tallafin Lamunin Dalibai
    Next Article ABU archaeology museum unveils student-curated exhibition

    Related Posts

    News

    Governor Radda Greets Sultan of Sokoto at 70, Says He’s a Bridge Builder

    August 24, 2026
    News

    COAS, JONATHAN, DEFENCE CHIEFS ADVANCE SECURITY–INDUSTRIAL GROWTH NEXUS AT NDC COURSE 34 GRADUATION LECTURE

    August 24, 2026
    News

    Governor Radda Celebrates NTA, NAN Chiefs on Tenure Renewal, Extols Tinubu

    August 24, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026289 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026241 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026223 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026165 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026159 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026154 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.