Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Shugaba Tinubu Ya Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur
    News

    Shugaba Tinubu Ya Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanSeptember 12, 20262 Mins Read
    FB IMG 1789241878847
    FB IMG 1789241878847

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya mika sakon ta’aziyyarsa bisa rasuwar tsohon gwamnan tsohuwar Jihar Gongola, fitaccen dan kasuwa kuma dattijon kasa, Alhaji Bamanga Muhammad Tukur, wanda ya rasu yana da shekaru 90.

    Shugaba Tinubu ya bayyana marigayin, wanda aka fi sani da Tafidan Adamawa, a matsayin babban jigo da ya taka muhimmiyar rawa a harkokin mulki, siyasa, masana’antu da kasuwanci. Tukur ya taba zama babban manajan Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya (NPA) daga 1975 zuwa 1982, kafin daga bisani ya zama gwamnan tsohuwar Jihar Gongola a shekarar 1983.

    Marigayin ya kuma rike mukamin Ministan Masana’antu a gwamnatin Janar Sani Abacha daga 1993 zuwa 1995, sannan ya jagoranci wasu manyan kamfanoni a bangaren masana’antu, noma, sufuri da kasuwanci. A fagen siyasa, ya zama Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa daga watan Maris 2012 zuwa Janairu 2014, yayin da a matakin Afirka ya taka rawa wajen bunkasa kasuwanci da hadin gwiwar tattalin arzikin nahiyar.

    Shugaba Tinubu ya bayyana Bamanga Tukur a matsayin mutum mai hangen nesa, karamci da kishin kasa, yana mai cewa Najeriya za ta yi kewar shawarwarinsa da jagorancinsa na uba. Ya mika ta’aziyya ga iyalan marigayin, Masarautar Fombina ta Adamawa, gwamnatin da al’ummar Jihar Adamawa da al’ummar kasuwanci da siyasa baki daya, tare da rokon Allah Ya gafarta masa kurakuransa, Ya ba shi Aljannar Firdausi, Ya kuma ba iyalansa hakurin jure wannan rashi.

    bamanga mourn pbat
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGovernor Radda Makes Stopover in Kazaure
    Next Article BAMANGA MUHAMMAD TUKUR (SEPTEMBER 1935 – SEPTEMBER 2026)

    Related Posts

    News

    GOVERNOR DAUDA LAWAL TO ATTEND UN GENERAL ASSEMBLY IN NEW YORK

    September 16, 2026
    News

    ZAMFARA FIRST LADY UNITES WITH NORTHERN GOVERNORS’ WIVES IN ADAMAWA TO DRIVE TRANSFORMATIVE HUMANITARIAN AID AND REGIONAL EMPOWERMENT

    September 16, 2026
    News

    Northern Governor’s wives forum support 1,200 vulnerable women in Adamawa.

    September 16, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026304 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026245 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026234 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026173 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026168 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026156 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.