Sabuwar Nigeria
Shugaban Ƙasan, ya kuma nemi yi malaman addini a Najeriya, Afirka da sauran sassan duniya da su ci gaba da anfani da muryoyinsu kan yaki da ta’addanci, garkuwa da mutane, da kuma amfani da addini wajen kashe-kashe da tashin hankali.
Shugaba Tinubu ya ce babu wata ibada ta gaskiya da za ta samu ci gaba ta hanyar zubar da jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
Shugaban Ƙasar ya yi wannan horon ne a ranar Lahadi a Kano, a cikin saƙon fatan alheri da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya isar a madadinsa a wajen babban Mauludin Shehu Ahmad Al-Tijani (RTA). Ya ce malaman addini na da muhimmiyar gudunmuwar da za su bayar wajen wayar da kan matasa, koyar da zaman lafiya, ilimin addini da kyawawan ɗabi’u, tare da yin kira ga shugabannin siyasa da su yi adalci da nuna tausayi.
Tinubu ya ce matsalolin da duniya ke fuskanta, da suka haɗa da yaƙe-yaƙe, matsin tattalin arziki, yunwa, ta’addanci da rikice-rikicen da ake haddasawa ta hanyar addini da ƙabilanci, sun ƙara nuna muhimmancin gudunmuwar da shugabannin addini za su bayar wajen wanzar da zaman lafiya.
Ya ce ɗariƙar Tijjaniyya, saboda yawan mabiyanta da hanyoyin sadarwarta a Afirka ta Yamma da Arewa, ta na da damar taimakawa wajen sasanta rikice-rikice, yaƙi da tsattsauran ra’ayi da jagorantar matasa zuwa tsarkin zuciya.
Shugaban Ƙasar ya kuma bayyana Najeriya a matsayin ƙasa mai matuƙar muhimmanci ga zaman lafiyar yankin saboda matsayinta a tsakanin kasashen Afirka ta Yamma, da Sahel, da Tafkin Chadi da Tekun Guinea. Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare ’yancin ’yan Najeriya na gudanar da addininsu, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da malaman addini da sarakunan gargajiya domin tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da mutunta juna.
Tinubu ya kuma yi ta’aziyyar marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya ce rashinsa ya yi matuƙar tasiri a taron, yana mai bayyana shi a matsayin malami, uba kuma mai fafutukar zaman lafiya da kyakkyawar fahimta. Ya ce hanya mafi kyau ta girmama Shehun ita ce a ci gaba da gadon ilimin Alƙur’ani, koyar da kyawawan ɗabi’u, bautar Allah, zaman lafiya da kula da jin daɗin al’ummar da ya bari.

