…Ta ce Gwamna na da karɓuwa a cikin jam’iyya da ma wajen jama’a
Ƙungiyar Pantamiyya Movement Brothers, ƙarƙashin jagorancin fitaccen mai fafutukar siyasa, Sanusi Hamisu Usman wanda aka fi sani da Ameer Sanusin-Gombe, ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Dan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar APC, Dr. Jamil Isyaku Gwamna, gabanin zaɓen 2027.
Ƙungiyar, wadda ke da Ko’odinatoci Sama da100 a dukkanin Akwatuna na ƙananan hukumomi 11 na jihar, ta ce goyon bayan da ta bai wa Dr. Gwamna ya samo asali ne daga irin karɓuwar da yake samu a cikin jam’iyyar APC da kuma a tsakanin al’umma baki ɗaya.
Da yake jawabi yayin wata ziyarar goyon baya da suka kai wa Dr. Gwamna, Ameer Sanusin-Gombe ya bayyana ganawar a matsayin mai muhimmanci kuma ta zo a kan lokaci, yana mai cewa ƙungiyar ta kuduri aniyar goyon bayan Dr. Jamil Isyaku Gwamna, wanda zai iya ci gaba da ayyukan ci gaban da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya assasa.
A cewarsa, gogewar siyasar Dr. Gwamna, kusancinsa da talakawa, da kuma karɓuwarsa a tsakanin ɓangarori daban-daban na jam’iyyar ne suka sa ya zama mafi dacewa da wannan nauyi.
“Mun zo ne domin nuna goyon bayanmu da jajircewarmu wajen ganin APC ta ci gaba da kasancewa a haɗe tare da samun nasara a 2027. Dr. Gwamna ya nuna tawali’u da kuma ƙwarewar tafiya da kowa,” in ji shi.
Wannan Na kunshe ne cikin wata sanarwar da Mai taimakawa Dr Jamil Isyaku Gwamna ta fuskar yada labarai, Ibrahim Sani shawai ya rabawa manema labarai.
Sanusin-Gombe ya kuma yi kira ga tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki, Farfesa Isa Ali Pantami, da sauran masu neman takara a APC da su haɗa kai da Dr. Gwamna domin amfanin jam’iyya da ci gaban jihar Gombe.
Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a jam’iyyar na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da gagarumar nasara ga APC a zaɓen gwamna da na shugaban ƙasa.
A nasa ɓangaren, Dr. Gwamna ya gode wa ƙungiyar Pantamiyya bisa fifita haɗin kan jam’iyya fiye da komai, yana mai bayyana ziyarar a matsayin alamar tsaftatacciyar siyasa da jajircewa wajen tabbatar da makomar APC a jihar.
Dan takarar gwamnan na APC ya tabbatar wa ‘yan jam’iyyar cewa zai rungumi shugabanci mai haɗa kai da kowa, wanda zai ba kowane ɓangare damar da ta dace, don a gudu tare a kuma tsira tare.
Ya kuma yi kira ga dukkanin tsoffin ‘yan takara da masu ruwa da tsaki da su ajiye bambance-bambancen da suka taso bayan zaɓen fidda gwani, su haɗa kai a matsayin iyali ɗaya domin ci gaba da ayyukan ci gaba da gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ke aiwatarwa.
Haka kuma, Dr. Gwamna ya sake jaddada aniyarsa ta samar da goyon baya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da sauran ‘yan takarar APC a zaɓen 2027, yana mai cewa haɗin kai da manufa ɗaya su ne ginshiƙan nasarar jam’iyyar a jihar Gombe.




