Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » 2027: PDP a Gombe: Jam’iyya ce wacce Bata da Ɗan Takarar Gwamnan, Jam’iya Ce Mai Cike da Rikici
    Politics

    2027: PDP a Gombe: Jam’iyya ce wacce Bata da Ɗan Takarar Gwamnan, Jam’iya Ce Mai Cike da Rikici

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJune 27, 20263 Mins Read
    FB IMG 1782591446508
    FB IMG 1782591446508

     

    Daga Anwar Pantami

    Yayin da zaɓukan shekarar 2027 ke ƙara matsowa, siyasar Najeriya na ƙara rikicewa, musamman a bangaren jam’iyyun adawa da ke fama da rashin tabbas da kuma rarrabuwar kawuna. A Jihar Gombe ne wannan matsala ta fi bayyana karara, inda jam’iyyar PDP ke cikin wani mummunan rikici da ya jefa ta cikin shakku kan ko za ta iya tsayawa da ɗan takara guda a zaɓen gwamna.

    Tsawon watanni, PDP a Gombe na fama da rikicin shugabanci mai tsanani, wanda ya samo asali daga yadda aka fitar da ɗan takarar gwamna ta wata hanya da ‘yan jam’iyya da dama ke ganin ba ta bi ka’ida ba. Wannan lamari ya ƙara dagula al’amura, musamman ganin cewa jam’iyyar ta dade tana kasa samar da tsayayyen shugabanci mai haɗa kai a jihar.

    Abin da ya fi ba wa magoya baya takaici shi ne yadda aka yi watsi da waɗanda suka shafe shekaru suna gina jam’iyyar tun daga tushe, aka maye gurbinsu da wani mutum da ake kallon kamar mai anfani da dama ne kawai. Farfesa Isa Ali Pantami, wanda tarihin sa da alaƙarsa da jam’iyyar ke jefa ayar tambaya kan amincinsa da kuma biyayyarsa ga manufofin PDP.

    Sai dai duk wannan cece-kuce ba ta kai girman tambayar da yanzu ke yawo a zukatan al’ummar Gombe ba: Shin PDP tana da sahihin ɗan takarar gwamna na 2027 kuwa?

    Wannan tambaya ba wai ta magana ce kawai ba; gaskiya ce da ke neman amsa.

    A wani lamari mai ɗaure kai, an ce akwai ɓangarori biyu na PDP a matakin ƙasa da suka bayar da takardun shaidar cin zaɓe ga mutane biyu daban-daban. Wani ɓangare da ake dangantawa da Ministan Babban Birnin Tarayya ya goyi bayan Pantami, yayin da wani ɓangaren kuma da ke ƙarƙashin halastaccen jagoranci na kwamitin Aminu Turaki ya bai wa Hon. Ahmed Yayari takardarsa. Yayari dai gogaggen ɗan siyasa ne, tsohon Shugaban Ma’aikata a gwamnatin Ibrahim Hassan Dankwambo, kuma ya taba zama Ma’ajin Kasa na jam’iyyar.

    Wannan abu da bai taba faruwa ba ya jefa magoya bayan jam’iyyar cikin rudani, takaici da rashin kwarin gwiwa. Tsarin ladabi da dimokuraɗiyyar cikin gida da PDP ke alfahari da su sun fara rugujewa a fili.

    Illolin wannan rikici suna da girma, kuma suna iya yin tasiri nan gaba. Ba zai yiwu jam’iyya ta shiga zaɓe da ‘yan takara biyu a kujerar guda ba. Wannan ba wai kawai kuskure ba ne, illa ce da za ta iya hallaka jam’iyyar gaba ɗaya.

    A wannan lokaci mai muhimmanci, PDP a Gombe na fuskantar barazanar zama ba komai a siyasa. Idan ba a dauki matakan gaggawa ba don sasanta rikicin, haɗa kan ‘yan jam’iyya, da kuma dawo da martabar tsarin ta, akwai yiwuwar jam’iyyar ta shiga zaɓen 2027 cikin rauni ko ma ba tare da ɗan takara ba.

    Kuma a siyasa, kamar yadda yake a rayuwa, babu gurbi da yake zama babu mai cikewa.

     

     

     

    gombe pdp rigingimun
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleNorth East Youths innovation summit showcases AI-driven solutions to governance
    Next Article PDP CRISIS DEEPENS IN GOMBE STATE

    Related Posts

    Politics

    Gombe LG polls: APC Guber candidate commends improved process, voter turn-out

    June 27, 2026
    Politics

    An Gudanar da Zaben kananan Hukumomin Jihar Gombe abin Zakkyau,cikin lumana

    June 27, 2026
    Politics

    PDP CRISIS DEEPENS IN GOMBE STATE

    June 27, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026244 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026231 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026183 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026149 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026149 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026136 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.