Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » “Gani Ya Kori Ji”: Ayarin Manema Labarai Sun Kai Ziyara kan Ayyukan Ban Ruwa Da Gidajen Renewed Hope a Kano
    News

    “Gani Ya Kori Ji”: Ayarin Manema Labarai Sun Kai Ziyara kan Ayyukan Ban Ruwa Da Gidajen Renewed Hope a Kano

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJuly 8, 20263 Mins Read
    FB IMG 1783501740538
    FB IMG 1783501740538

    Sabuwar Nigeria.

    Ayarin shirin “Gani Ya Kori Ji” ƙarƙashin jagorancin Babban Mai taimakawa Shugaban kasa na Musamman ga kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, sun ci gaba da rangadin duba manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar ta biyu da ziyarar wasu manyan ayyuka a Jihar Kano.

    Shirin, wanda aka ƙaddamar domin bai wa ’yan Najeriya damar gani da idanunsu irin ayyukan da Shirin Renewed Hope da gwabnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa, na nufin duba, sa ido da kuma tantance ayyukan da aka kammala da kuma waɗanda ake ci gaba da yi, maimakon dogaro da shaci fadi Kawai..

    A ranar farko ta Ziyarar, ayarin sun isa Aikin noman rani na Challawa da ke Ƙaramar Hukumar Karaye, inda suka duba yadda aikin ke gudana da kuma irin gudummawar da ake sa ran zai bayar wajen bunƙasa noma da samar da wadataccen abinci.

    Daga nan Kuma Ayarin zakakuran manema labaran zarce zuwa Renewed Hope City da ke Janguza a Kano, inda suka zagaya kashi na farko da na biyu na aikin gidajen gwamnatin tarayya.

    Wannan aikin yana daga cikin manyan shirye-shiryen gwamnatin tarayya na samar da gidaje masu inganci da sauki domin rage ƙarancin gidaje a ƙasar, tare da samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa tattalin arziki.

    Rahotanni sun nuna cewa aikin ya ƙunshi fiye da gidaje 1,000. An kammala Kashi na farko da ya ƙunshi gidaje 325, waɗanda ke jiran ƙaddamarwa, yayin da ake ci gaba da aikin kashi na biyu wanda zai ƙara kusan gidaje 698.

    Aikin ya ƙunshi gidaje iri-iri domin biyan bukatun iyalai daban-daban, ciki har da rukunin gidaje bene da na ƙasa masu dakuna uku,you, da huɗu , hudu da kuma masu dakuna biyar, biyar.

    Jagoran ayarin Malam Abdulaziz Abdulaziz ya ce shirin “Gani Ya Kori Ji” zai ci gaba da kai ziyara zuwa wasu manyan ayyukan gwamnatin tarayya a jihohin Arewacin Najeriya domin bai wa jama’a damar ganin ci gaban da ake samu ƙarƙashin manufofin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

    Ya ce manufar shirin ita ce tabbatar da gaskiya da bayyana ayyukan gwamnati kai tsaye ga al’umma ta hanyar kai su wuraren da ake aiwatar da su domin su gani da idanunsu da Kuma kararwa ga jamaa.

    FB IMG 1783501734042
    FB IMG 1783501734042
    FB IMG 1783501727496
    FB IMG 1783501727496
    FB IMG 1783501720268
    FB IMG 1783501720268
    FB IMG 1783501711760
    FB IMG 1783501711760
    FB IMG 1783501705898
    FB IMG 1783501705898
    FB IMG 1783501687176
    FB IMG 1783501687176

     

     

     

    day gani ya ji kori second
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGwamna restates Commitment to ‘Gombe First’ Agenda, as PDP chieftains join APC.
    Next Article NADCEL 2026: Nigerian Army Conducts Free Medical Outreach in Okrika Community

    Related Posts

    News

    GOVERNOR DAUDA LAWAL TO ATTEND UN GENERAL ASSEMBLY IN NEW YORK

    September 16, 2026
    News

    ZAMFARA FIRST LADY UNITES WITH NORTHERN GOVERNORS’ WIVES IN ADAMAWA TO DRIVE TRANSFORMATIVE HUMANITARIAN AID AND REGIONAL EMPOWERMENT

    September 16, 2026
    News

    Northern Governor’s wives forum support 1,200 vulnerable women in Adamawa.

    September 16, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026304 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026245 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026234 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026173 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026168 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026156 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.