Sabuwar Nigeria.
Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga maaikatan kafafen yada labarai su riƙa tantance gaskiyar bayanai kafin wallafawa Ko sanar da jamaa.
Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Abdulaziz Abdulaziz, Shi ne ya gabatar DA wannan bukatar wajen wani muhimmin taron yada labarai da aka yi a kano.
Abdulaziz Abdulaziz ya ce bunƙasar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa muhimmin alamari be da Ke bukatar amincewa da Samun haɗin kai a tsakanin gwamnati, da kafafen yaɗa labarai da kuma al’umma.
Babban Mai Taimakawa Shugaban kasan ya bayyana cewa tilas ne kafofin yada au rika laakari da yanayin kasa da sa ra ana duban bakin gatari a ayyukan da suke Yi din amfanin zaman lafiya da walwala da kuma ci gaban kasa.
A cewarsa taron ya haɗa shugabanni, ‘yan jarida, masu ƙirƙirar Ko rubuta abubuwan da ake wallafawa a shafukan sada zumunta, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna yadda za a ƙarfafa alaƙar gwamnati da jama’a ta hanyar gaskiya, riƙon amana da ɗabi’ar aikin jarida.
Abdulaziz Abdulaziz ya ce taron da aka Yi wa taken “ Yarjejeniya a tsakanin alumma da gwabnatin, kamanta gaskiya,nauyin da ya rataya a wuyar gwabnati da Yan jarida,da kuma tsarin gudanar da aikin jarida “,wato “Government-Citizen Accord: Accountability, Responsibility and Ethical Media Practice” ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar sake samun kyakyawan Alaska da amincewa tsakanin gwamnati da al’umma.
Ya bayyana cewa gwamnati na da alhakin buɗe ƙofofin samun bayanai, yayin da al’umma ke da nauyin tabbatar da gaskiya kafin yaɗa bayanai da kuma riƙe gwamnati da alhakin ayyukanta cikin lumana.
Ya ce kafafen yaɗa labarai tankar tsani be a tsakanin gwamnati da jama’a, yana mai cewa ingantaccen aikin jarida da tabbatar da sahihancin labarai na taimakawa wajen samun zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa.
Abdulaziz ya kuma jaddada cewa masu tasiri a shafukan sada zumunta sun zama sabbin masu jan ragamar yaɗa bayanai, don haka wajibi ne su riƙa tantance gaskiyar bayanai kafin wallafawa.
“A yau, saƙon da aka wallafa na iya haifar da fata ko kuma tayar da husuma cikin ɗan lokaci. Don haka bai kamata neman farin jini ko yawan masu kallo ya zama sanadin jefa ƙasa cikin rikici ba,” Kamar yadda ya ce.
Ya ƙara da cewa yayin da zaɓen shekarar 2027 ke ƙaratowa, akwai buƙatar masu amfani da shafukan sada zumunta Na zamani su ɗauki kansu a matsayin masu tabbatar da zaman lafiyar al’umma, tare da gyara kura-kurensu idan sun faru.
Ya bayyana cewa a wani ɓangare na shirye-shiryen taron, an horas da sama da mutum 100 daga cikin masu goyon bayan jam’iyyar APC da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan dabarun yaɗa bayanai da bayyana manufofi da nasarorin gwamnati yadda ya kamata.
Haka kuma ya ce an ƙaddamar da shirin Gani-Ya-Kori-Ji, wanda zai zagaya jihohin Arewacin Najeriya domin duba da kuma haska ayyukan ci gaba da gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi suka aiwatar, musamman waɗanda jamaa ba su San da su ba.
Abdulaziz ya ce taron ya nuna irin ƙudirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare ‘yancin faɗin albarkacin baki, ƙarfafa tattaunawa da kuma bunƙasa dimokuraɗiyya.
Ya bayyana cewa an tsara taron ne domin bai wabma su mabambantan ra’ayoyi da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na Arewacin Najeriya damar tattaunawa kan makomar hulɗar gwamnati da jama’a.
A ƙarshe, ya yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa amincewa da karɓar baƙuncin taron, yana mai cewa Kano ta ci gaba da kasancewa cibiyar siyasa, kasuwanci da tattaunawa a Najeriya
Ya buƙaci mahalarta taron su fito da sabbin dabarun da za su inganta tsarin gudanar da mulki a bayyane, da ƙarfafa ɗabi’ar aikin jarida da kuma inganta alaƙar gwamnati da al’umma.





