Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Ci gaban Jihar Gombe da Muradun al’umma, su ne a gabana…….Dakta Jamil Gwamna.
    Politics

    Ci gaban Jihar Gombe da Muradun al’umma, su ne a gabana…….Dakta Jamil Gwamna.

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanMay 18, 20262 Mins Read
    FB IMG 1779086124422
    FB IMG 1779086124422

     

    Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Gombe, Dakta Jamil Gwamna (Sardaunan Gombe), ya sake jaddada ƙudirinsa na ganin ya hada kan al’umma guri guda don ƙara haɓaka ci gaban Jihar.

    Dakta Gwamna ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnatinsa da yardar Allah za ta kasance mai kula da jama’a tare da bai wa kowa dama, inda babu wanda za a bari a baya saboda asali, jinsi ko matsayinsa a cikin al’umma.

    Wata sanarwar da Mai taimakawa Dr Jamil Isyaku Gwamna Akan harkokin yada labarai Ibrahim Sani Shawai ya bayar, ya ce Dr Jamil Isyaku Gwamna Ya yi alƙawarin samar da gwamnati inda kowace murya za ta kasance mai muhimmanci kuma kowane ɗan ƙasa zai taka rawa a harkokin mulki daidai da matsayinsa.

    Sardaunan Gombe ya kuma miƙa hannu na neman haɗin kai ga sauran masu neman takara don a kasance tsintsiya ɗaya maɗaurinki ɗaya. Dakta. Gwamna ya bayyana su a matsayin abokan tafiya wajen ci gaba maimakon abokan takara.

    Ya ce, “Dukkanmu muna da manufa guda ɗaya, wato ci-gaban Jihar Gombe. Ina miƙa hannun haɗin kai ga dukkan masu neman takara, don mu gudu tare mu kuma tsira tare.

    A ɗaya ɓangaren, Gwamna ya yaba wa nasarorin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, yana mai cewa gwamnatinsa ta kafa tubali mai ƙarfi na ci-gaba a fannoni daban-daban na rayuwa.

    Ya jaddada cewa shugabancinsa zai mayar da hankali wajen ƙarfafa waɗannan nasarori tare da hanzarta ci-gaba a fannoni masu muhimmanci kamar ilimi, lafiya, gina ɗan Adam, gine-gine, noma da ƙarfafa matasa.

    Dakta Gwamna ya kuma sake tabbatar da ƙudirinsa na daidaita Jihar Gombe da Ajandar “Sabunta Fata” na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

    Ya bayyana cewa hakan zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙi, samar da ayyukan yi da kuma inganta rayuwar al’ummar Jihar Gombe baki ɗaya.

    Ɗan takarar APCn ya yi alƙawarin kafa gwamnati mai sauraron al’umma da aiki tuƙuru da kuma samar da sakamako na zahiri ga jama’a.

    A ƙarshe Dakta Gwamna ya yi kira ga al’ummar Jihar Gombe da su rungumi haɗin kai, ci-gaba da shugabanci nagari.

    “Wannan shi ne lokacinmu na zaɓar haɗin kai maimakon rarrabuwar kawuna, ci-gaba maimakon siyasa da shugabancin da zai yi wa jama’a aiki na gaskiya.”

     

    burinmu ci Gavan gombe ne Sardaunan
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleNIGERIAN NAVY UNCOVERS SUSPECTED STAGING CAMP, RECOVERS AMMUNITION AND EXPLOSIVE-MAKING MATERIALS IN RIVERS–BAYELSA CREEK AXIS
    Next Article ‘Why ABU was awarded N40m nominal prize despite being 1st place winner of JAMB award’

    Related Posts

    Opinion

    Real Legacy Is Building People Who Build the Nation: The Human Capital Philosophy of Dr Jamil Gwamna

    September 17, 2026
    Opinion

    ABDULRAHMAN: The Sardauna I Have Known for Three Decades

    September 17, 2026
    Politics

    2027: Darika Sect Endorses Tinubu, Radda, Pledges Support for APC

    September 17, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026304 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026245 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026234 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026175 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026168 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026158 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.