Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » DAN TAKARAR GWABNAN JIHAR GOMBE KARKASHIN APC, DR JAMIL ISYAKU GWAMNA YA SHA ALWASHIN SHIGA KOWANE LUNGU NA JIHAR DON NEMAN KURI’UN JAMAA.
    Politics

    DAN TAKARAR GWABNAN JIHAR GOMBE KARKASHIN APC, DR JAMIL ISYAKU GWAMNA YA SHA ALWASHIN SHIGA KOWANE LUNGU NA JIHAR DON NEMAN KURI’UN JAMAA.

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJune 1, 20262 Mins Read
    FB IMG 1780307848768
    FB IMG 1780307848768

    Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Gombe, Dokta Jamil Isyaku Gwamna, ya bayyana aniyarsa ta zagaya dukkan ƙananan hukumomin jihar domin neman kuri’ar al’umma kai tsaye, duk da irin gagarumin goyon bayan da yake samu daga sassa daban-daban na jama’a a faɗin jihar.

    Wannan na kunshe ne cikin sanarwar manema labarai da Ibrahim Sani Shawai,mai taimakawa Dr Jamil Isyaku Gwamna ta fuskar yada labarai ya baiwa manema labarai.

    Sanarwar ta ce Dr. Gwamna ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Gombe, inda ya jaddada cewa dimokuraɗiyya na buƙatar kusanci da jama’a da kuma neman amincewarsu kai tsaye.

    Ya ce, duk da cewa ya na samun cikakken goyon baya daga yan jam’iyyun adawa, ‘yan kasuwa, ‘Kungiyoyi, malamai da sauran masu ruwa da tsaki, hakan ba zai hana shi sauka ƙasa domin ci gaba da tuntuɓar al’umma ba, domin a cewarsa, neman kuri’a daga bakin jama’a shi ne ginshiƙin nasara mai ɗorewa.

    “Duk da irin tarin goyon bayan da nake samu daga bangarori daban-daban, hakan ba zai sa na zauna ba. Zan shiga lungu da sako a duk faɗin jihar Gombe domin ganawa da al’umma, sauraron damuwarsu, da kuma neman amincewarsu da kuma kuri’arsu,” in ji Dokta Gwamna.

    Ya kuma tabbatar da cewa zai gudanar da yaƙin neman zaɓensa cikin tsafta, lumana da mutunta juna, tare da mai da hankali kan manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’ummar Jihar Gombe gaba ɗaya.

    Dokta Gwamna ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da ba shi goyon baya tare da fitowa kwansu da kwarkwatarsu domin amfani da haƙƙinsu na zaɓe a lokacin da ya dace, yana mai jaddada aniyarsa ta kawo ci gaba mai ma’ana idan aka ba shi dama ya jagoranci jihar.

    A karshe Dokta Jamil Gwamna ya yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya CON Kan Irin ci gaban daya kawo a fannoni daban- daban na rayuwa a Jihar Gombe, tare da alkawarin ci gaba daga inda ya tsaya.

     

    gwamna Isyaku jamil lungu
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleNIGER STATE PILGRIMS’ WELFARE BOARD ATTENDS POST ARAFAT BRIEFING IN MAKKAH.
    Next Article The Price of Integrity: Why Mustapha Muhammad’s Honest Act Deserves More Than Applause*

    Related Posts

    Politics

    MHR ZANNAN BUNGUDU EARMARKS 50 MILLION NAIRA FOR PROJECT EXECUTION IN KUYAMBANA WARD OF DANSADAU EMIRATE

    June 7, 2026
    Politics

    GOMBE APC GUBERNATORIAL CANDIDATE INAUGURATES SARDAUNA VOLUNTEERS GROUP

    June 7, 2026
    News

    GOMBE STATE APC GUBERNATORIAL CANDIDATE DR JAMIL ISYAKU GWAMNA CONGRATULATES EMIR OF GOMBE ON 12 ON THE THRONE.

    June 6, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026226 Views

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026224 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026167 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026138 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026134 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026131 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.