Dan takarar gwabnan jihar Gombe karkashin tutar Janiyyar APC, Dr Jamil Isyaku Gwamna ya nuna Godiyarsa marar adadi ga al’ummar Birin Fulani dake ƙaramar hukumar Nafada bisa ziyarar da suka kawo mini domin gaisuwar Sallah, murna da kuma bayyana cikakken goyon baya ga tafiyar da muka ɗora kan turbar ci gaba.
Sanarwar da Dan takarar gwabnan ya sanyawa hannu ta ce Wannan ziyara mai ma’ana ta zo ne ƙarƙashin jagorancin Hon. Usman Jahun, Mai bai wa Mai Girma Gwamnan Jihar Gombe shawara kan harkokin karkara, kuma tsohon Kwamishina, a gwamnatin Mai Girma Gwamna, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, CON.
Hakika, wannan gagarumar goyon baya da kuka nuna ba kawai abin alfahari ba ne, alama ce ta amincewa, haɗin kai da kuma ƙudurin al’umma na ganin an samu ci gaba mai ɗorewa. Wannan ya ƙara tabbatar mana da cewa tafiyar da muka fara tafiya ce ta gaskiya, ta ci gaba, kuma ta jama’a baki ɗaya.
Ina tabbatar muku cewa za mu ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen kare muradun al’umma, tare da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar kowa da kowa, ba tare da wariya ba.
Ina matuƙar godiya bisa wannan karamci da goyon baya. Allah Ya saka muku da alheri, Ya ba mu nasara, Ya kuma riƙe hannayenmu wajen ciyar da jiharmu gaba cikin zaman lafiya, haɗin kai da cigaba mai ma’ana.






