Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Gani da Ido Na Ayyukan Raya Kasa da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ke aiwatarwa a Kano. Aikin Kano Northern Bypass zai rage cunkoso tare da bunƙasa tattalin arziki
    News

    Gani da Ido Na Ayyukan Raya Kasa da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ke aiwatarwa a Kano. Aikin Kano Northern Bypass zai rage cunkoso tare da bunƙasa tattalin arziki

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJuly 6, 20263 Mins Read
    FB IMG 1783340134428
    FB IMG 1783340134428

    Sabuwar Nigeria.

    A ci gaba da rangadin manyan ayyukan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, Ke gudanarwa a Jihar Kano a ƙarƙashin shirin Arewa Media Summit, ayarin masu yaɗa labarai sun kai ziyara zuwa aikin hanyar Bayan Gari da Ake ginawa a arewacin Kano (Northern Bypass,) wanda ake sa ran zai sauya fasalin zirga-zirga da harkokin kasuwanci a jihar.

    Rangadin, wanda Ofishin Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, ya shirya, na da nufin bai wa mahalarta taron cikakken haske da Kuma Gani da Ido kan muhimman ayyukan gwamnatin tarayya da ke gudana a Arewacin Najeriya.

    Aikin Kano Northern Bypass, mai tsawon kusan kilomita 38, ya taso ne daga kan hanyar Kano zuwa Hadejia zuwa hanyar Kano zuwa Katsina, inda ake sa ran zai rage cunkoson manyan motoci da ke ratsawa cikin birnin Kano.

    Masana sun bayyana cewa idan aka kammala aikin, zai taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirgar kayayyaki da fasinjoji, rage bata lokacin da Ake Yi a hanyoyin shiga kano da kuɗaɗen sufuri, tare da bunƙasa harkokin masana’antu da kasuwanci a yankunan da hanyar ta ratsa.

    Haka kuma, ana sa ran aikin zai ƙara jawo sabbin masu zuba jari da samar da ayyukan yi ga matasa, musamman a yankunan Zaura, Dawanau, Tarda da sauran al’ummomin da ke kusa da hanyar.

    Shugabannin shirin Arewa Media Summit sun bayyana cewa rangadin na da muhimmanci wajen bai wa ‘yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta damar gani da ido da kuma fahimtar irin ci gaban da ake samu a ƙarƙashin Ajandar Renewed Hope ta Shugaba Tinubu.

    Sun ce samar da sahihan bayanai da rahotanni ma su dogaro da hujjoji za su taimaka matuka wajen ƙarfafa fahimtar jama’a game da ayyukan raya ƙasa da ake aiwatarwa a yankin Arewa da ma Najeriya baki ɗaya.

    Ana sa ran taron Arewa Media Summit da za a gudanar a ranar 6 ga watan Yuli, 2026, a Coronation Hall da ke Fadar Gwamnatin Jihar Kano, zai haɗa manyan ‘yan jarida, masu tasiri, masana da masu ruwa da tsaki domin tattauna gudunmuwar da kafafen yaɗa labarai Za su bayar wajen bunƙasa ci gaban Arewa.

    FB IMG 1783340130056
    FB IMG 1783340130056
    FB IMG 1783340125735
    FB IMG 1783340125735
    FB IMG 1783340119467
    FB IMG 1783340119467
    FB IMG 1783340110614
    FB IMG 1783340110614
    FB IMG 1783340105193
    FB IMG 1783340105193
    FB IMG 1783340099700
    FB IMG 1783340099700

     

    a kano ayyukan da gani Ido tinubu
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleAKWA IBOM POLICE COMMAND CRACKS DOWN ON CULTISM, DRUG ABUSE, AND VANDALISM; SUSPECTS ARRESTED, EXHIBITS RECOVERED
    Next Article KDSPWB COMMENCES REGISTRATION FOR 2027 HAJJ.

    Related Posts

    News

    Governor Inuwa Yahaya Moves to Deepen Federal Partnership on Livestock Development, Meets Minister Mukhtar Maiha

    July 30, 2026
    News

    Gov. Yusuf Condoles Sokoto Governor, Sultan, and People of Sokoto Over the Death of Former Finance Minister

    July 30, 2026
    News

    IGP DISU HOSTS DEPOWA PRESIDENT AT FORCE HEADQUARTERS, ADVOCATES ENHANCED WELFARE FOR PERSONNEL

    July 30, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026275 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026235 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026212 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026159 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026156 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026151 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.