Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » ‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin layin dogo na Kano-Maradi zai sauya tattalin arzikin Arewa — Jami’ai
    News

    ‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin layin dogo na Kano-Maradi zai sauya tattalin arzikin Arewa — Jami’ai

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJuly 8, 20263 Mins Read
    FB IMG 1783543760219
    FB IMG 1783543760219

     

    Sabuwar Nigeria.

    A ci gaba da rangadin ‘Gani Ya Kori Ji’ na manyan ayyukan gwamnatin tarayya a Arewacin Najeriya, Ayarin yan jarida da ke rangadi tare da Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, sun kai ziyara aikin gina layin dogo na zamani na da ya tashi daga Kano–Maradi domin duba yadda aikin ke gudana tare da samun cikakken bayani daga jami’an da ke kula da shi.

    A yayin ziyarar, Manajan Wurin Aikin ya bayyana wa ayarin cewa aikin na tafiya yadda aka tsara, yana mai nuna kwarin gwiwar cewa idan aka ci gaba da aiki a wannan mataki, ana sa ran kammala shi kafin ƙarshen shekarar nan.

    Ya ce layin dogon na daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da aka tsara domin inganta hanyoyin sufuri, bunƙasa kasuwanci da haɗa tattalin arzikin Najeriya da na Jamhuriyar Nijar.

    An bayyana wa mahalarta rangadin cewa babban layin dogon zai tashi daga Kano zuwa Maradi mai tsawon kusan kilomita 285, yayin da wani reshe mai tsawon kusan kilomita 108 zai haɗa Kano da Dutse a Jihar Jigawa. Da zarar an kammala aikin, zai sauƙaƙa zirga-zirgar fasinjoji da kayayyaki, rage cunkoson manyan tituna, da kuma ƙarfafa harkokin kasuwanci tsakanin Najeriya da Nijar tare da buɗe sabbin damarmaki ga jihohin Kano, Jigawa, Katsina da sauran yankunan da ke makwabtaka da su.

    Jami’an aikin sun kuma bayyana cewa layin dogon zai haifar da dubban guraben ayyukan yi kai tsaye da kuma a fakaice ga injiniyoyi, masu sana’o’in hannu, ma’aikatan sufuri, ‘yan kasuwa, kamfanoni da sauran masu ruwa da tsaki. Haka kuma, zai ƙara ƙarfafa masana’antu, jawo masu zuba jari, bunƙasa darajar noma tare da bai wa manoma damar kai amfaninsu cikin sauƙi zuwa manyan kasuwanni.

    Masu aikin jaridar da ke cikin shirin ‘Gani Ya Kori Ji’ sun bayyana cewa irin wannan rangadi na ba su damar gani da ido kan yadda manyan ayyukan gwamnatin tarayya ke gudana maimakon dogaro da jita-jita. Sun ce aikin layin dogo na Kano–Maradi wata muhimmiyar shaida ce ta ƙudirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na aiwatar da Ajandar Sabunta Fata (Renewed Hope Agenda) ta hanyar gina ingantattun ababen more rayuwa, ƙarfafa haɗin kan yankuna da bunƙasa tattalin arzikin Arewacin Najeriya da ƙasar baki ɗaya.

    FB IMG 1783543788069
    FB IMG 1783543788069
    FB IMG 1783543782795
    FB IMG 1783543782795
    FB IMG 1783543764620
    FB IMG 1783543764620
    FB IMG 1783543769231
    FB IMG 1783543769231

     

     

     

    dogo gani ji kano kori layin maradi ya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleCOAS HONOURED AS “OMU UDO 1 OF EBONYI,” AS STAKEHOLDERS DEEPEN CIVIL–MILITARY SYNERGY FOR NATIONAL SECURITY
    Next Article NIGERIAN ARMY EXPANDS FOOTPRINT IN SOUTH-EAST AS COAS, GOVERNORS FLAG OFF STRATEGIC 120-BED MEDICAL CENTRE

    Related Posts

    News

    Hippopotamus ravages farmlands in Adamawa Communities,Farmers seek intervention.

    July 29, 2026
    News

    Adamawa government relaxes curfew in war torn lamurde local government.

    July 29, 2026
    News

    NAHCON URGES 2026 HAJJ PILGRIMS WHO HAVE COMPLAINTS OR COMMENTS ABOUT SERVICES RENDERED BY INDIVIDUALS OR INSTITUTIONS TO FORWARD SAME FOR APPROPRIATE ACTION.

    July 28, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026272 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026235 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026210 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026158 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026155 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026150 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.