Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Najeriya (NNGF) ta bayyana matuƙar baƙin cikinta game da rasuwar tsohon Ministan Kuɗi kuma Sardaunan Sakkwato, Alhaji Abubakar Alhaji, wanda ya rasu a safiyar jiya Alhamis a Abuja.
A cikin wani saƙon ta’aziyya, Shugaban Ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya bayyana marigayi Alhaji Abubakar Alhaji a matsayin ƙwararren ma’aikacin gwamnati kuma dattijo mai ƙima, wanda ya ba da gudummawa ta fannoni daban-daban don ci gaban ƙasa a shekaru da dama da ya shafe yana hidima cikin gaskiya da amana.
Ya tuno cewa Alhaji Abubakar Alhaji ya riƙe manyan muƙamai, ciki har da Ministan Tsare-tsare na Ƙasa sannan daga baya ya zama Ministan Kuɗi a lokacin mulkin Janar Ibrahim Babangida, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara manufofin tattalin arzikin ƙasar nan.
Baya ga aikinsa na minista, an naɗa shi Babban Jakadan Najeriya a Birtaniya a shekarar 1992, muƙamin da ya riƙe tare da yiwa Najeriya hidima da cikakkiyar girmamawa.
Shugaban ƙungiyar gwamnonin na Arewan ya kuma yaba da halayyar marigayin da kuma zuriya ta gari da ya fito, ta Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, yana mai cewa bayan barinsa aikin gwamnati, ya ci gaba da kasancewa jigo mai kula da ɗabi’u da al’adun Daular Sakkwato da kuma kare martabarsu.
Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, rasuwar Alhaji Abubakar Alhaji babban rashi ne ba kawai ga iyalansa da al’ummar Jihar Sakkwato ba, har ma ga Arewa da daukacin Najeriya, waɗanda suka amfana sosai daga ɗimbin gogewa, jagoranci na gari, da kuma shawarwarinsa masu fa’ida ga ƙasa.
A madadin Gwamnonin Jihohin Arewa 19, Gwamna Inuwa Yahaya ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, Sarkin Musulmi, Mai Martaba Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, da ƙasar Sakkwato, da Gwamnati da al’ummar Jihar Sakkwato, da kuma dokacin ‘yan Najeriya dake cikin jimamin rashin wannan babban dattijo.
Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta wa marigayi Alhaji Abubakar Alhaji kurakuransa, ya kuma saka masa da Aljanna Firdausi saboda gudummawar da ya bayar ga al’umma.

