Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar Maulidin Annabi Muhammad (SAWA), inda ya bukace su da su yi koyi da kyawawan halayen Manzon Allah.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, Shugaban ya ce bai kamata Maulidi ya tsaya kan bikin ranar haihuwar Annabi kawai ba, sai an yi amfani da lokacin wajen yin nazari, addu’a da koyon darussan rayuwarsa.
Tinubu ya ce Musulmi su yi ƙoƙari su riƙa bin koyarwar Annabi Muhammad, yana mai cewa rayuwarsa na ɗauke da manyan darussa na ibada, juriya, haƙuri da sadaukar da kai.
Shugaban ya kuma bukaci malaman addini da su yi amfani da lokacin Maulidi wajen yi wa ƙasar addu’a, tare da jan hankalin mabiyansu kan su mayar da darussan rayuwar Annabi a aikace wajen nuna kishin ƙasa.
Haka kuma, ya bukaci Musulmin da ke gudanar da bikin Maulidi su tallafa wa mabukata da masu rauni, musamman a cikin wannan lokaci.
Shugaban ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’a domin samun nasara kan matsalolin tsaro da sauran ƙalubalen da ke addabar wasu sassan ƙasar.

