Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Shugaba Tinubu ya umarci jami’an tsaro su ceto mutanen da aka sace a jihar Neja
    Security

    Shugaba Tinubu ya umarci jami’an tsaro su ceto mutanen da aka sace a jihar Neja

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 25, 20262 Mins Read
    FB IMG 1787687368775
    FB IMG 1787687368775

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci rundunar sojojin Najeriya, da rundunar ‘yan sanda, da Hukumar DSS da sauran hukumomin tsaro da leƙen asiri da su fara aikin haɗin gwiwa domin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a wani sabon harin satar mutane da ya faru a Jihar Neja.

    A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, Shugaba Tinubu ya bayyana matuƙar ɓacin ransa kan sacewa da kashe fararen hula da miyagun masu laifuka suka yi a jihar.

    Shugaban ya ce waɗanda suka kai harin kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, “makiyan zaman lafiya ne kuma makiyan bil’adama”, yana mai cewa ba za a bar su su tsere wa hukunci ba.

    Ya kuma mika ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda aka kashe, yana roƙon Allah Ya jiƙansu, Ya kuma bai wa iyalansu ƙarfin jure wannan babban rashi.

    Tinubu ya ce al’ummar da lamarin ya shafa ba su kaɗai ba ne, yana mai cewa ƙasa baki ɗaya na tare da su a cikin wannan mawuyacin hali.

    Ya ce gwamnatin tarayya ba za ta huta ba har sai an dawo da ’ya’ya, iyaye mata da maza da aka yi garkuwa da su cikin aminci.

    Shugaban Ƙasar ya kuma umarci shugabannin hukumomin tsaro da su riƙa ba shi rahoto kai-tsaye kan yadda aikin ceto ke gudana har sai an tabbatar da inda duk mutanen da aka sace suke.

    “Ta’addanci ba zai tsoratar da Najeriya ba. Za mu kare al’ummarmu, mu kare garuruwanmu, kuma mu tabbatar da mutuncin rayuwar ɗan Adam,” in ji shi.

    Shugaba Tinubu ya kuma bayyana cewa addu’arsa na tare da al’ummar Jihar Neja a wannan lokaci na ƙalubale, yana mai cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bai wa gwamnatin jihar dukkan goyon bayan da ake buƙata domin aikin ceto, agaji da ƙara tsaro.

    Sabuwar Nigeria

    agencies direct kidnapped niger pbat rescue security victims
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleMaulidi: Tinubu ya Bukaci alummar Musulmi su yi koyi da koyarwar Annabi (SAW)
    Next Article Governor Radda Announces Personal Funding for Zawiyya Guest House

    Related Posts

    Security

    *Nigeria Targets Defence Self-Reliance, Deepens Industrial Partnership with Türkiye

    August 26, 2026
    Security

    OPERATION ENDURING PEACE INTENSIFIES ONGOING OPERATIONS AND RESCUE KIDNAPPED VICTIMS IN PLATEAU STATE

    August 26, 2026
    Security

    Tudun Wada DPO Visits FUE Zaria, Assures VC of Police Support

    August 26, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026291 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026241 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026223 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026166 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026159 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026154 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.