Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci rundunar sojojin Najeriya, da rundunar ‘yan sanda, da Hukumar DSS da sauran hukumomin tsaro da leƙen asiri da su fara aikin haɗin gwiwa domin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a wani sabon harin satar mutane da ya faru a Jihar Neja.
A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, Shugaba Tinubu ya bayyana matuƙar ɓacin ransa kan sacewa da kashe fararen hula da miyagun masu laifuka suka yi a jihar.
Shugaban ya ce waɗanda suka kai harin kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, “makiyan zaman lafiya ne kuma makiyan bil’adama”, yana mai cewa ba za a bar su su tsere wa hukunci ba.
Ya kuma mika ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda aka kashe, yana roƙon Allah Ya jiƙansu, Ya kuma bai wa iyalansu ƙarfin jure wannan babban rashi.
Tinubu ya ce al’ummar da lamarin ya shafa ba su kaɗai ba ne, yana mai cewa ƙasa baki ɗaya na tare da su a cikin wannan mawuyacin hali.
Ya ce gwamnatin tarayya ba za ta huta ba har sai an dawo da ’ya’ya, iyaye mata da maza da aka yi garkuwa da su cikin aminci.
Shugaban Ƙasar ya kuma umarci shugabannin hukumomin tsaro da su riƙa ba shi rahoto kai-tsaye kan yadda aikin ceto ke gudana har sai an tabbatar da inda duk mutanen da aka sace suke.
“Ta’addanci ba zai tsoratar da Najeriya ba. Za mu kare al’ummarmu, mu kare garuruwanmu, kuma mu tabbatar da mutuncin rayuwar ɗan Adam,” in ji shi.
Shugaba Tinubu ya kuma bayyana cewa addu’arsa na tare da al’ummar Jihar Neja a wannan lokaci na ƙalubale, yana mai cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bai wa gwamnatin jihar dukkan goyon bayan da ake buƙata domin aikin ceto, agaji da ƙara tsaro.
Sabuwar Nigeria

