Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Murmushin Samun Nasara
    Opinion

    Murmushin Samun Nasara

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanMay 15, 20264 Mins Read
    FB IMG 1778873012359
    FB IMG 1778873012359

     

    Daga Abba Anwar

    Ni dai tuntuni na san irin kyakkyawan wakilci nagari da kuma ayyukan alherin da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Maigirma Sanata Barau I Jibrin, CFR, PhD, yake yi, ina da tabbacin cewa jiga-jigan siyasa na Kano ta Arewa, ba za su taba bari abin ya kwaranye a banza ba.

    Ita fa adawa ko samun sabani a siyasa ba haram ba ne, a tsarin dimokuraɗiyya. Kuma an fi ganin irin wannan a wuraren da a ke da dandazon jagorori, kuma masu kishin al’ummar su. Dan kowannensu ya na da irin nasa karfin da tasiri a wajen mutanen sa.

    Misali yanzu a Kano ta Arewa, akwai shi kansa Sanata Barau din, akwai tsohon gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, CON, akwai Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Murtala Sule Garo, akwai tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Abdullahi T. Gwarzo, sannan akwai dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Bichi, kuma shugaban kwamitin raba arzikin kasa na majalisar, da kuma wasu jiga-jigai daga Kano ta Arewan.

    Dukkanin jagororin nan da na ambata, kowannensu sarki ne a cikin mutanen sa. Dukkansu su na bukatar junansu, dan samun nasarar jam’iyyar a dukkan matakai, musamman a jiha.

    Samun nasarar sulhu da a ka samu tsakanin Sanata Barau da kuma ATM Gwarzo, kan takarar Sanata a zabe mai zuwa na 2027, ba karamar nasara ba ce, wacce ta samu ne saboda hobbasar wadannan jiga-jigai. Shi kuma Maigirma Gwamna Kano, Abba Kabir Yusuf, ba karamin shugabanci nagari ya nuna ba wajen tsayin daka da ya yi na tabbatuwar wannan abin. Tabbas ya nuna kwarewa da hangen nesa a mulki da siyasa.

    Haka nan bayan samun wannan daidaituwa na ji wata hira da Sanata Barau ya yi da ‘yan jarida, har na ji ya yabawa mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, wato Maigirma Ibrahim Masari. Hakan ya nuna mana irin kokarin da Masarin ya yi wajen ganin an yi maganin kowace irin baraka da ka iya kawo cikas. Dan haka ya zama wajibi shi ma a yaba masa.

    Ni fa a gani na, wannan abin da Masarin ya yi, ya na nuni da irin damuwa da jihar da shugaban kasa ya yi ne, wajen samun nasarar jam’iyyar APC da kuma cigaban jihar. Ban dai ga wajen da Masarin ya je ya yi irin wannan aiki ba da ya hada da mai babban mukami irin na Barau ba. Ni dai ban gani ba, ban kuma sani ba.

    A dalilin wannan cigaban da a ka samu kuma, na san Maigirma Sanata zai kara fahimtar cewar ashe dai jama’arsa na matukar jin dadin yadda yake kawo musu ci gaba a mazabarsa ta Kano ta Arewa. Daga ciki kuwa har da wadanda a ke wa kallon abokan adawarsa, a da kafin sulhu, na siyasa.

    Samun nasara da kuma Sanata Barau, kamar yan tagwaye ne. Daya ya na manne da dayan. Tabbas irin wannan tsarin namu na dimokuraɗiyya ya na bukatar jajirtattun jagorori irin sa. Ga kishin al’umma, ga sanin me mazabarsa da yankin sa na arewa ke bukata.

    Hadewar Barau da Garo da Gwarzo waje daya, shine yake kara tabbatarwa da kowa cewar, har yanzu dai jam’iyyar APC a jihar Kano ta fi karfi da tasiri da mamaya, a Kano ta Arewa. Sama da ragowar shiyyoyin jihar. Wato Kano ta Tsakiya, wacce na fito daga ciki, da kuma Kano ta Kudu. Su jagororin Kano ta Arewa din sun fi ragowar jagororin kishin jam’iyyar da kuma neman dukkan hanyoyin samun nasarar jam’iyyar. In gaya maka dalili? Zaben 2023.

    Bayan wannan sulhu da a ka samu, ni a ganina, yanzu ba wai dan ta-fadi-gasassa ba ne kawai zai koma daga baya ya na kara kulla wata wutar gaba ba, illa shaidan. Duk kankantantar mutum a jam’iyya kuwa. Kuma duk girman sa. Babban abin dadin ma kawai shine, Allah Ya hore mana tsayayyen gwamna. Mai adalci. Saboda haka duk wasu kulle – kulle za su tashi a banza ne.

    Anwar ya rubuto daga Kano

    Juma’at, 15 ga Watan Mayu, 2026

    murmushin nasara samun
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGwarzo Condemns Bandit Attacks in Kano Communities, Urges Stronger Security Measures
    Next Article Gombe Deepens Agricultural, Economic Partnerships with FCDO, Propcom+

    Related Posts

    Opinion

    Consensus, Primaries and Anti-Party Activity: The Quiet Fault Lines in Nigeria’s Political Parties.

    May 26, 2026
    Opinion

    DRAMATIC EVICTION IN SOKOTO: HOW A TRIBUNAL ORDER ENDED A BITTER ONE-YEAR BATTLE OVER BAZZA AREA PROPERTY SOKOTO

    May 26, 2026
    Opinion

    NOBODY CAN BELIEVE HUNGRY PRESIDENTIAL ASPIRANT PLEDGING SINGLE TERM TO MAINTAIN 8YRS DOUBLE TERM ROTATION FOR THE NIGERIAN SET UP.

    May 26, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026225 Views

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026222 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026165 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026133 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026133 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026128 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.