Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, CON, a matsayin babban rashi ga Jihar Jigawa da Nijeriya baki ɗaya.
Shettima ya ce marigayi Sarkin ya kasance daga cikin sarakunan gargajiya da suka sadaukar da shekaru masu yawa wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ilimi, ci gaban al’umma da ƙarfafa haɗin kan ƴan ƙasa.
Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a Jihar Jigawa, lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayin da Masarautar Gumel, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin tarayya.
Marigayi Sarkin Gumel na 16 ya rasu a birnin Alkahira na ƙasar Masar a ranar 3 ga Satumba, 2026, bayan shafe kusan shekaru 46 yana mulkin masarautar. Ya hau karagar mulki ne a ranar 16 ga Disamba, 1980.
Mataimakin Shugaban Ƙasan ya ce za a tuna da marigayi Sarkin ne saboda tsawon mulkinsa, tare da hikima, zaman lafiya da kishin al’ummar da ya nuna wajen gudanar da shugabancinsa.
Ya bayyana shi a matsayin uba, mai haɗa kan jama’a, kuma mai bayar da shawarwari, wanda hikimarsa ta taimaka wajen hidimtawa al’umma da ƙasa tsawon kusan rabin ƙarni.
Shettima ya ce duk da cewa mulkin marigayin ya gudana a lokacin da Nijeriya ta fuskanci sauye-sauyen siyasa da zamantakewa da dama, ya ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, ilimi, karatun addinin Musulunci da zaman tare cikin lumana.
Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama marigayi Sarkin, musamman bisa gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma.
Shettima ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi, tare da ba iyalansa, Masarautar Gumel da al’ummar Jihar Jigawa haƙurin jure wannan babban rashi.

