A ci gaba da aiwatar da ƙudirin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na dawo da cikakken tsaro a faɗin Najeriya, Hukumar Kula da Ƙananan Makamai da Makamai Masu Sauƙin Sarrafawa ta Ƙasa (NCCSALW), ƙarƙashin Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA), ta lalata makamai 2,809 da jami’an tsaro suka kwato daga hannun masu laifi. Wannan mataki ya sake nuna cewa gwamnati ba wai tana yaƙar masu aikata laifi kaɗai ba, har ma tana tabbatar da cewa makaman da aka ƙwace ba za su sake komawa hannun miyagu ba.
A wajen aikin lalata makaman da aka gudanar a Barikin Muhammadu Buhari da ke Giri, Abuja, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, wanda Dr. Dennis Otuaro ya wakilta, ya bayyana cewa yaƙi da yawaitar makamai ba bisa ƙa’ida ba na daga cikin manyan ginshiƙan dabarun gwamnatin Tinubu na magance ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami, tada ƙayar baya da sauran matsalolin tsaro. Ya ce duk makamin da aka kwato kuma aka lalata yana nufin an kawar da wata babbar barazana ga rayuka da dukiyoyin al’ummar Najeriya.
Ribadu ya kuma aika da gargaɗi ga masu safarar makamai da masu aikata laifuka cewa gwamnatin tarayya ba za ta yi sassauci da duk wani da ke taka rawa wajen yaɗa makamai ba bisa ƙa’ida ba. A cewarsa, duk makamin da jami’an tsaro suka kwato za a lalata shi domin hana sake komawarsa hannun masu tayar da zaune tsaye.
Shi ma Darakta Janar na NCCSALW, DIG Johnson Babatunde Kokumo, ya ce tun bayan kafa cibiyar a shekarar 2021, an yi nasarar kwato tare da lalata kusan makamai 19,000, lamarin da ke nuna irin ci gaban da ake samu a yaƙin da gwamnati ke yi da masu aikata laifuka.
Wannan wani muhimmin ci gaba ne da ke ƙara tabbatar da cewa Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba magana ba ce kawai, aiki ne da ke haifar da sakamako. Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da matsa kaimi wajen ƙwato makamai daga hannun masu laifi, alamu na nuna cewa Najeriya na ci gaba da ɗaukar ingantattun matakai domin samar da ƙasa mai zaman lafiya, tsaro da ci gaba ga kowa
sabuwar Nigeria






