Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa kan rasuwar Sarkin Zamfaran Zurmi, Mai Martaba Alhaji Bello Sulaiman, wanda ya rasu a ranar Litinin, bayan shafe shekaru biyar a kan karagar mulkin masarautar.
A cikin wata sanarwa da mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Laraba, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Zurmi, Gwamnatin Jihar Zamfara da al’ummar jihar, da kuma daukacin masarautun Najeriya.
Shugaban ya bayyana marigayin a matsayin basaraken da ake girmamawa, wanda ya jagoranci al’ummarsa cikin hikima, mutunci da jajircewa a wani lokaci mai matuƙar wahala. Ya ce marigayin ya nuna ƙwarewar jagoranci wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi masarautar Zurmi.
Tinubu ya ce Sarkin ya kasance jigo wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da juriya a tsakanin al’ummarsa, yana mai cewa shawarwarinsa masu hikima da ƙoƙarinsa na samar da zaman lafiya sun taimaka ba kawai ga Masarautar Zurmi ba, har ma da Jihar Zamfara da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin Arewa maso Yamma.
Shugaban Ƙasar ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kurakuransa, Ya saka masa da alheri kan ayyukan da ya yi, Ya kuma ba shi Aljannar Firdausi. Ya kuma roƙi Allah Ya bai wa iyalansa da duk waɗanda rasuwar ta shafa haƙuri da ƙarfin zuciyar jure wannan babban rashi.

