Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Alhaji Abubakar Alhaji
    News

    Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Alhaji Abubakar Alhaji

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJuly 31, 20261 Min Read
    IMG 20260730 WA0018
    IMG 20260730 WA0018

    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhini kan rasuwar tsohon Ministan Kuɗi kuma fitaccen ɗan siyasa, kuma jami’in gwamnati, Alhaji Abubakar Alhaji, wanda ya rasu yana da shekaru 85.

    A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Alhamis, Tinubu ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin fitattun masu hidimar ƙasa, wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a manyan muƙaman gwamnati.

    Shugaban ya ce marigayi Sardaunan Sakkwato ya yi fice a fannin gudanar da mulki, tare da nuna ƙwarewa wajen tafiyar da harkokin kuɗi da kuma diflomasiyya, lamarin da ya ba da gagarumar gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da siyasar Najeriya.

    Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, Majalisar Masarautar Sakkwato da daukacin iyalan gidan sarautar bisa wannan babban rashi.

    Haka kuma, ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Sakkwato, al’ummar jihar, da abokan hulɗa da ɗaliban da marigayin ya koyar tare da jagoranta a sassa daban-daban na ƙasar.

    Shugaban ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa Alhaji Abubakar Alhaji, Ya saka masa da Aljannatul Firdausi saboda hidimomin da ya yi wa ƙasa da al’umma, sannan Ya bai wa iyalansa da al’ummar Sakkwato haƙurin jure wannan babban rashi.

    alh taaziyya tinubu
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Sardaunan Sakkwato, Alhaji Alhaji
    Next Article KDSG COMMENDS FG FOR ADOPTION OF THE STATE HOUSEHOLD MAPPING MODEL AS NATIONAL FRAMEWORK FOR TACKLING OUT OF SCHOOL CHILDREN CHALLENGE.

    Related Posts

    News

    ZAMFARA FARMERS CRY OUT AS QUEALA BIRDS RAVAGES FARMS IN BAKALORI IRRIGATION AREAS.

    July 31, 2026
    News

    RECONSTRUCTION OF MANDO -BIRNIN GWARI ROAD TO COMMENCES SOON.

    July 31, 2026
    News

    Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Sardaunan Sakkwato, Alhaji Alhaji

    July 31, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026275 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026235 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026213 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026159 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026156 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026151 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.