Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA…..
    Opinion

    ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA…..

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanMay 28, 20263 Mins Read
    FB IMG 1779996742945
    FB IMG 1779996742945

    Ibrahim Sani Shawai.

    Sardaunan Gombe, Dakta Jamil Isyaku Gwamna mutum ne da a yanzu haka ludayinsa ke kan dawo, bisa la’akari da yadda yake ci gaba da samun karɓuwa a saƙo da lungu na Jihar Gombe.

    Karɓuwarsa da irin goyon bayan da jama’a ke ci gaba da nuna wa Dakta Jamil Gwamna, hujja ce ƙarara da ke nuna irin ƙwarewarsa a siyasa, hangen nesansa a harkoki na rayuwa, gogewarsa a harkokin gudanarwa da kuma haƙurinsa da tawali’unsa na musamman.

    Waɗannan kyawawan halaye ne suka sa ya shiga zukatan talakawa, tare da tabbatar da shi a matsayin jagora mai iya haɗa kan al’umma, kare nasarorin dimokraɗiyya, samar da shugabanci na kowa da kowa da kuma ciyar da muradun al’ummar Jihar Gombe gaba.

    Babu shakka, irin ƙaruwar farin jini da ƙarfi da ke tattare da takararsa ta Gwamna a ƙarƙashin tutar Jam’iyyar APC na nuna irin amincewa da jama’a ke da ita ga shugabancinsa mai hangen nesa.

    Idan aka yi la’akari da yanayin siyasar da ake ciki a yanzu da kuma yadda magoya bayan jam’iyyu da masu zaɓe ke ci gaba da nuna ƙwarin guiwa, babu ko ja ina da cikakken yaƙinin cewa jam’iyyar APC tana kan turbar samun gagarumar nasara mai tarihi a zaɓen da ke tafe a Jihar Gombe, in sha Allah.

    Dakta Jamil, wanda ake wa laƙabi da “Kowa Naka”, mutum ne mai sauƙin kai da son jama’a. Mutum ne da ba shi da abokin faɗa, domin ɗabi’arsa ita ce lumana, hikima da mutunta kowa ba tare da nuna banbanci ba. Ba ya yin magana sai ya yi nazari tare da auna kalamansa cikin natsuwa da basira.

    A tsawon shekarun da ya shafe yana aiki, a ɓangare ɗaya kuma da mu’amala da jama’a, ya nuna cikakkiyar ƙwarewa wajen tafiyar da al’amura cikin adalci da gaskiya. Wannan ne ya sa mutane da dama ke kallonsa a matsayin mutum mai cika alƙawari, mai kishin ci gaban al’umma da kuma shugaba da ke da manufar kawo sauyi mai amfani ga rayuwar jama’a.

    A yau, matasa, dattawa, mata da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar Gombe na ci gaba da bayyana goyon bayansu gare shi, saboda sun yarda cewa yana da abin da ake buƙata domin kai Jihar Gombe zuwa wani matsayi mafi girma na ci gaba mai ma’ana.

    Haƙiƙa, idan aka ci gaba da tafiya a kan wannan tsari na haɗin kai, haƙuri da kyakkyawar manufa, babu abin da zai hana Dakta Jamil Isyaku Gwamna samun nasara tare da rubuta sabon tarihin siyasa a Jihar Gombe.

     

    gombe gwamna jamil
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleCOAS CHARGES TROOPS OF OPERATION SAVANNAH SHIELD TO DECISIVELY ROUT CRIMINAL ELEMENTS
    Next Article Kebbi Governor Pays Hadaya for State Pilgrims in Saudi Arabia*

    Related Posts

    News

    Gombe APC Gubernatorial Candidate Mourns Renowned Islamic Scholar, Malam Abubakar Sadiq (Pharmacy)

    June 5, 2026
    Politics

    Dan takarar gwabnan jihar Gombe karkashin tutar Janiyyar APC,Dakta Jamil Isyaku Gwamna Ya Buƙaci Al’ummar Gombe: Su Karɓi Katin Zaɓe.

    June 5, 2026
    News

    Tinubu Flags- off Landmark N1.245 Trillion Gombe – Biu Super highway Dualization Project

    June 4, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026226 Views

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026224 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026167 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026138 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026134 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026131 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.