Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa kudurin tabbatar da dorewar tsarin ba da lamunin karatu ga daliban Najeriya.
NELFUND ta ce Shugaban Kasar ya umurci a karkatar da kudaden da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da sauran laifukan Tattalin Arziki (EFCC) ta kwato, zuwa asusun NELFUND domin karfafa tallafin lamunin karatu.
A cikin wata sanarwa da Daraktar Sadarwa ta NELFUND, Mrs Oseyemi Oluwatuyi, ta fitar ranar 19 ga Agusta, 2026, asusun ya kuma yi maraba da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) kan tura ribar da ba a karba ba daga Capital Market Trust Fund da Dormant Account Trust Fund zuwa NELFUND.
NELFUND ta ce matakan za su taimaka wajen samar da ingantaccen tushe na kudaden da za su ci gaba da tallafa wa shirin lamunin dalibai yayin da yawan masu neman tallafin ke karuwa.
A cewar asusun, zuwa watan Agustan 2026, NELFUND ta riga ta fitar da sama da Naira biliyan 322 ga dalibai, daga cikin masu neman lamunin karatu sama da miliyan 1.6 da aka gabatar.
Shugaban Hukumar Gudanarwar NELFUND, Jim Ovia, ya bayyana godiya ga Shugaba Tinubu bisa ci gaba da goyon baya da amincewar da yake bai wa asusun, yana mai cewa hakan ya kara karfin kudurin gwamnatin na tabbatar da cewa rashin kudi bai zama dalilin hana wani dan Najeriya samun ilimi mai zurfi ba.
Shi ma Manajan Daraktan NELFUND, Akintunde Sawyer, ya ce sabon kudurin Shugaban Kasa ya nuna irin muhimmancin da gwamnatin ke bai wa ilimi, tare da kokarin gina tsarin ba da lamunin karatu mai dorewa.
Sawyer ya tabbatar da cewa NELFUND za ta ci gaba da amfani da dukkanin kudaden da aka damka mata cikin gaskiya da rikon amana, domin amfanin daliban Najeriya.
NELFUND ta ce sabon tsarin samar da kudade zai kara wa Gwamnatin Tarayya karfin fadada shirin da kuma kai lamunin karatu ga karin daliban Najeriya da suka cancanta.


