Yayin da shirye-shiryen zaɓuka ke ƙara ƙaratowa, fitaccen ɗan siyasa kuma jagoran tafiyar “Gombe Ce a Gabanmu”, Dakta Jamil Isyaku Gwamna, ya buƙaci ɗaukacin al’ummar Jihar Gombe da su tabbatar sun karɓi katin zaɓensu domin su taka muhimmiyar rawa wajen tsara makomar jiharsu.
A cikin sanarwar manema labarai da Ibrahim Sani shawai mai taimakawa Dr Jamil Isyaku Akan harkokin yada labarai ya ce Dakta Jamil ya bayyana cewa katin zaɓe shi ne ginshiƙin dimokraɗiyya kuma babban makamin da talaka ke da shi wajen tabbatar da an samu shugabanci nagari, adalci da ci gaba mai ɗorewa.
Ya ce lokaci ya yi da al’ummar Gombe za su nuna kishin jiharsu ta hanyar fitowa domin karɓar katin zaɓensu, ya ce domin babu wani ci gaba da za a samu idan jama’a ba su yi amfani da haƙƙinsu na zaɓe ba.
“Manufar Gombe Ce a Gabanmu ba ta mutum ɗaya ba ce. Manufa ce ta kowa da kowa; ta matasa, mata, manoma, makiyaya, ma’aikata, malamai, ‘yan kasuwa da dukkan al’ummar jihar Gombe masu burin ganin jiharmu ta samu ci gaba a fannoni daban-daban,” in ji Dakta Jamil.
Ya ƙara da cewa ci gaban da jama’a ke fata a ɓangarorin ilimi, lafiya, noma, samar da ayyukan yi, kasuwanci da ababen more rayuwa zai samu ne kawai idan al’umma suka kasance cikin masu yanke hukunci ta hanyar amfani da katin zaɓensu.
Gwamna ya kuma yi kira ga magoya baya da masu ruwa da tsaki a dukkan ƙananan hukumomin jihar da su zama jakadun wayar da kai, su rinƙa ƙarfafa iyalai, abokai da maƙwabta su karɓi katin zaɓensu tare da kiyaye zaman lafiya da mutunta dokokin ƙasa.
“Muna kira ga kowa da kowa da ya tashi tsaye ya karɓi katin zaɓensa. Katin zaɓe shi ne muryarka, ƙarfinka da makaminka wajen ci gaba da gina Gombe da muke mafarki. Idan muna son Gombe ta kasance ta farko, dole ne mu fara da amfani da haƙƙinmu na zaɓe.” Inji Dokta Gwamna.
A karshe Dokta Gwamna Ya yi addu’ar Allah Ya ci gaba da dafawa Gwamna Inuwa Yahaya Ya kuma ba al’ummar jihar Gombe haɗin kai, zaman lafiya da hikimar zaɓar shugabannin da za su kai jihar zuwa mataki na gaba.

