Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » ‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin Shinfida bututun iskar gas na Ajaokuta, zuwa Kaduna ,zuwa Kano,AKK ya kai kashi 95% Na kanmaluwa
    News

    ‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin Shinfida bututun iskar gas na Ajaokuta, zuwa Kaduna ,zuwa Kano,AKK ya kai kashi 95% Na kanmaluwa

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanJuly 8, 20263 Mins Read
    FB IMG 1783539884756
    FB IMG 1783539884756

    Sabuwar Nigeria.

    Wannan aikin dai muhimmi ne da zai inganta samar da lantarki da kakkafa masana’antu da Kuma bunkasa tattalin arzikin Arewacin Kasar nan

    A rana ta uku na rangadin ‘Gani Ya Kori Ji’ na manyan ayyukan gwamnatin tarayya a Arewacin Najeriya, Ayarin masu aikin yada labarai da ke rangadi tare da Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, Sun kai ziyara zuwa aikin Shinfida bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), ɗaya daga cikin manyan ayyukan samar da makamashi da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.

    Wannan ga ni da Ido, ya bai wa wakilan Ayarin damar ganin yadda aikin ke gudana da kuma samun cikakken bayani daga jami’an da ke kula da aikin.

    A yayin ziyarar, Ayarin sun fara isa Block Valve Station 19 da ke ƙauyen Rahma Wali a Ƙaramar Hukumar Makarfi ta Jihar Kaduna, inda jami’an aikin suka bayyana cewa aikin ya kai kusan kashi 95 cikin 100 na kammaluwa.

    Sun nuna kwarin gwiwar cewa da zarar an ƙaddamar da aikin, zai samar da iskar gas mai ɗorewa ga tashoshin samar da wutar lantarki da masana’antu, lamarin da zai rage kuɗin makamashi, ƙara samar da lantarki da kuma buɗe ƙofofin kafa sabbin masana’antu a Arewacin ƙasar.

    Jami’an sun bayyana cewa aikin, wanda aka fara a zamanin gwamnatin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, na ci gaba da samun cikakken goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata (Renewed Hope Agenda).

    Sun ce wannan ya nuna ƙudirin gwamnatin tarayya na kammala manyan ayyukan more rayuwa da ke da tasiri kai tsaye ga bunƙasar tattalin arziki da ci gaban ƙasa.

    An kuma yi wa Ayarin bayanin cewa bututun iskar gas na AKK mai tsawon kusan kilomita 614 zai haɗa yankunan da ake da wadataccen iskar gas a kudancin Najeriya da jihohin Arewa, tare da samar da ingantaccen makamashi ga masana’antu, kamfanonin sarrafa kayayyaki da sauran harkokin kasuwanci.

    Baya ga haka, aikin ya samar da dubban guraben ayyukan yi kai tsaye da kuma a fakaice a lokacin gini, kuma ana sa ran zai ƙara samar da ɗimbin ayyukan yi bayan fara aiki sakamakon sababbin masana’antu da harkokin kasuwancin da za su bunƙasa a yankunan da bututun ya ratsa.

    Masu aikin jaridar da ke cikin shirin ‘Gani Ya Kori Ji’ sun bayyana cewa ziyartar aikin ta ƙara musu fahimtar muhimmancin shirin ga makomar tattalin arzikin Arewa.

    Sun ce aikin ba kawai bututun iskar gas ba ne, amma wata babbar gada ce ta bunƙasa masana’antu, ƙarfafa samar da makamashi, jawo masu zuba jari da samar da ci gaba mai ɗorewa.

    Sun kuma bayyana aikin a matsayin wata babbar shaida ta ƙoƙarin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na amfani da manyan ayyukan more rayuwa wajen inganta rayuwar al’umma da dora tattalin arzikin Najeriya a Kan tafarki mai dorewa.

    FB IMG 1783540558401
    FB IMG 1783540558401
    FB IMG 1783539906035
    FB IMG 1783539906035
    FB IMG 1783539897565
    FB IMG 1783539897565
    FB IMG 1783539890532
    FB IMG 1783539890532
    FB IMG 1783539884756
    FB IMG 1783539884756
    FB IMG 1783539878945
    FB IMG 1783539878945
    gani da Ido nigeria sabuwar
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGOV UBA SANI HAS BEEN COMMENDED FOR EXECUTING IMPACTFUL DEVELOPMENT PROJECTS IN THE STATE.
    Next Article COAS PASSES OUT ANOTHER 3,000 RECRUITS, SUSTAINS MASSIVE RECRUITMENT DRIVE TO STRENGTHEN NATIONAL DEFENCE

    Related Posts

    News

    NAHCON URGES 2026 HAJJ PILGRIMS WHO HAVE COMPLAINTS OR COMMENTS ABOUT SERVICES RENDERED BY INDIVIDUALS OR INSTITUTIONS TO FORWARD SAME FOR APPROPRIATE ACTION.

    July 28, 2026
    News

    Kotun Daukaka Kara ta Soke hukuncin babbar kotun tarayya da ta nemi hukumar zabe ta Soke rajistan Janiyyar ADC da wasu jamiyyun siyasa Hudu.

    July 28, 2026
    News

    NIGER STATE MIN. OF LANDS GENERATES ABOUT N5 BILLION. …BOOSTS POWER & RENEWABLE ENERGY

    July 28, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026272 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026235 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026210 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026158 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026155 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026150 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.