Da sunan Allah Maɗaukakin Sarki, Mai ba da rai kuma Mamallakin dukkan iko, Wanda Yake bayar da mulki da ɗaukaka ga wanda Yake so, Ina miƙa dukkan yabo, godiya da ɗaukaka gare Shi bisa nuna mana wannan rana mai albarka.
Ina matuƙar jin daɗi da kaskantar da kai bisa amincewar da aka nuna mini ta hanyar zaɓe na a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC gabanin zaɓen 2027. Da cikakken sanin nauyin alhaki da jajircewa, ina karɓar wannan babban aiki na ɗaukar tutar jam’iyyarmu mai girma ta APC a zaɓen gwamna mai zuwa.
Ina miƙa godiya ta musamman ga jagoran jam’iyyar mu a Jihar Gombe, Mai Girma Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, bisa nagartaccen jagoranci, hikima ta siyasa, da jajircewarsa wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyya da jihar. A ƙarƙashin gwamnatinsa, Jihar Gombe ta samu gagarumin ci gaba a fannoni kamar ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, noma, tsaro da bunƙasa rayuwar al’umma.
Wadannan nasarori sun ba jam’iyyar mu ƙarfi da kwarin gwiwa yayin da muke shirin tunkarar zaɓen 2027. APC a Jihar Gombe a yau tana da haɗin kai, tsari mai kyau, kuma a shirye take don ci gaba da kyakkyawan shugabanci.
Ina kuma godiya ga shugabannin APC a matakai daban-daban, masu ruwa da tsaki, ‘yan takara, magoya baya da dukkan ‘yan jam’iyya bisa sadaukarwa da gudunmawarsu.
Zaben fidda gwani da aka gudanar ya nuna cewa APC jam’iyya ce mai gaskiya, haɗin kai, da mutunta dimokuraɗiyya. Wannan nasara ce ga dukkan ‘yan APC.
Ga abokan takara na, ina gode muku bisa nuna ƙwarewa da haƙuri. Yanzu lokaci ne na haɗuwa domin ci gaba da gina Gombe mai ƙarfi da haɗin kai.
Ga al’ummar Jihar Gombe, ina sane cewa wannan amana taku ce. Ina alƙawarin zama mai gaskiya, mai kusanci da jama’a, da kuma yin aiki da adalci ga kowa ba tare da la’akari da bambance-bambance ba.
Burina shi ne gina gwamnati mai haɗa kowa, wadda za ta ba kowa damar taka rawa wajen ci gaban jihar mu.
Turbar da muka dosa a yanzu, na buƙatar sadaukarwa, haƙuri da haɗin kai. Ina da yakinin cewa tare, za mu kai Jihar Gombe ga matakai mafi girma.
Da taimakon Allah da goyon bayan jama’a, muna da yakinin samun nasara a shekarar 2027 tare da ci gaba da gina kan tubalin da aka kafa.
Na gode, Allah Ya albarkaci Jihar Gombe da Nijeriya baki ɗaya.
Sa hannu:
Dr. Jamil I. Gwamna
Ɗan takarar Gwamna, APC, Jihar Gombe

