Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Jawabin karbar Sakamakon Zaben Fidda Gwani Na Takarar Gwamnan Jihar Gombe A Jam’iyyar APC
    Politics

    Jawabin karbar Sakamakon Zaben Fidda Gwani Na Takarar Gwamnan Jihar Gombe A Jam’iyyar APC

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanMay 22, 20263 Mins Read
    FB IMG 1779457349955
    FB IMG 1779457349955

     

    Da sunan Allah Maɗaukakin Sarki, Mai ba da rai kuma Mamallakin dukkan iko, Wanda Yake bayar da mulki da ɗaukaka ga wanda Yake so, Ina miƙa dukkan yabo, godiya da ɗaukaka gare Shi bisa nuna mana wannan rana mai albarka.

    Ina matuƙar jin daɗi da kaskantar da kai bisa amincewar da aka nuna mini ta hanyar zaɓe na a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC gabanin zaɓen 2027. Da cikakken sanin nauyin alhaki da jajircewa, ina karɓar wannan babban aiki na ɗaukar tutar jam’iyyarmu mai girma ta APC a zaɓen gwamna mai zuwa.

    Ina miƙa godiya ta musamman ga jagoran jam’iyyar mu a Jihar Gombe, Mai Girma Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, bisa nagartaccen jagoranci, hikima ta siyasa, da jajircewarsa wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyya da jihar. A ƙarƙashin gwamnatinsa, Jihar Gombe ta samu gagarumin ci gaba a fannoni kamar ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, noma, tsaro da bunƙasa rayuwar al’umma.

    Wadannan nasarori sun ba jam’iyyar mu ƙarfi da kwarin gwiwa yayin da muke shirin tunkarar zaɓen 2027. APC a Jihar Gombe a yau tana da haɗin kai, tsari mai kyau, kuma a shirye take don ci gaba da kyakkyawan shugabanci.

    Ina kuma godiya ga shugabannin APC a matakai daban-daban, masu ruwa da tsaki, ‘yan takara, magoya baya da dukkan ‘yan jam’iyya bisa sadaukarwa da gudunmawarsu.

    Zaben fidda gwani da aka gudanar ya nuna cewa APC jam’iyya ce mai gaskiya, haɗin kai, da mutunta dimokuraɗiyya. Wannan nasara ce ga dukkan ‘yan APC.

    Ga abokan takara na, ina gode muku bisa nuna ƙwarewa da haƙuri. Yanzu lokaci ne na haɗuwa domin ci gaba da gina Gombe mai ƙarfi da haɗin kai.

    Ga al’ummar Jihar Gombe, ina sane cewa wannan amana taku ce. Ina alƙawarin zama mai gaskiya, mai kusanci da jama’a, da kuma yin aiki da adalci ga kowa ba tare da la’akari da bambance-bambance ba.

    Burina shi ne gina gwamnati mai haɗa kowa, wadda za ta ba kowa damar taka rawa wajen ci gaban jihar mu.

    Turbar da muka dosa a yanzu, na buƙatar sadaukarwa, haƙuri da haɗin kai. Ina da yakinin cewa tare, za mu kai Jihar Gombe ga matakai mafi girma.

    Da taimakon Allah da goyon bayan jama’a, muna da yakinin samun nasara a shekarar 2027 tare da ci gaba da gina kan tubalin da aka kafa.

    Na gode, Allah Ya albarkaci Jihar Gombe da Nijeriya baki ɗaya.

    Sa hannu:

    Dr. Jamil I. Gwamna

    Ɗan takarar Gwamna, APC, Jihar Gombe

    amsar gombe Jawabin sakamakon zabe
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleLAST BATCH OF KADUNA INTENDING PILGRIMS DEPARTS MADINA FOR MAKKAH THIS FRIDAY.
    Next Article Governor Yusuf Constitutes 13-Member Committee for 3rd Anniversary Celebration

    Related Posts

    Opinion

    Real Legacy Is Building People Who Build the Nation: The Human Capital Philosophy of Dr Jamil Gwamna

    September 17, 2026
    Politics

    2027: Darika Sect Endorses Tinubu, Radda, Pledges Support for APC

    September 17, 2026
    Politics

    2027 : Christian Youths endorse Haske of APM for Adamawa gov’ship seat.

    September 17, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026304 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026245 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026234 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026175 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026168 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026158 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.