Daga Imrana Abdullahi
.Ministan ma’aikatar Gidaje da bunkasa yankunan karkara na Tarayyar Najeriya Injiniya Muttaqha Rabe Darma, ya bayyana cewa dukkan abubuwan da yake yi duk domin taimakawa al’umma ne ta yadda mafi yawa daga ciki za su gamsu.
Ministan ya ce hakika ko a yanzu jama’ar suna ta gamsuwa sakamakon ci gaban da suke sa mu ta fuskar irin abubuwan da ake yi.
“Muna yi wa Allah madaukakin Sarki godiya ko a yanzu mutane sun karbi duk abin da ake yi da hannu biyu biyu kuma mu tsakanin mu da Allah muna yi ne domin taimakawa al’umma”.
Amma ya kara da cewa duk da hidima ga al’umma abu ne mai wahala amma a koda yaushe ya na yin kokarin ganin ya hidimtawa jama’ar domin taimako saboda Allah madaukakin Sarki, don haka za mu kara kokarin yin abin da muke aikata wa

