Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Shugaba Tinubu ya ta ya Shettima murnar cika shekaru 60
    News

    Shugaba Tinubu ya ta ya Shettima murnar cika shekaru 60

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanSeptember 2, 20262 Mins Read
    FB IMG 1788333168184
    FB IMG 1788333168184

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, murnar cika shekaru 60 a ranar 2 ga Satumba, inda ya bayyana shi a matsayin amintaccen abokin aiki da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Borno da Najeriya hidima.

    A cikin saƙon taya murnar, Shugaba Tinubu ya taya matar Shettima, Nana, da ’ya’yansa, iyalansa da abokan siyasa murnar wannan gagarumin matsayi. Ya bayyana Shettima a matsayin ɗan kishin ƙasa mai jajircewa, haƙuri da sadaukarwa, tare da yabawa irin rawar da ya taka a harkar banki da kuma lokacin da yake Gwamnan Jihar Borno.

    Tinubu ya ce Shettima ya nuna jajircewa, ƙwazo da tausayi wajen inganta rayuwar al’umma a matsayinsa na Gwamnan Borno, sannan daga bisani a matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya. Ya kuma yaba masa bisa biyayyarsa ga jam’iyyar APC da kuma goyon bayan da yake bai wa gwamnatin tarayya wajen aiwatar da ajandar Renewed Hope.

    Shugaban ya bayyana cewa a matsayinsa na Shugaban Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa (NEC), Shettima ya taka muhimmiyar rawa wajen daidaita manufofin tattalin arziki da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi. Ya ce mutunta kundin tsarin mulki, cibiyoyin dimokuraɗiyya, tattaunawa da tuntuba da Shettima ke yi sun taimaka wajen ƙarfafa shugabanci nagari.

    Tinubu ya gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasar bisa amincinsa da goyon bayansa, yana mai cewa zai ci gaba da aiki tare da shi wajen cika alkawuran Renewed Hope ga ’yan Najeriya. Ya kuma yi masa addu’ar Allah Ya ba shi lafiya, hikima da tsawon rai, tare da ci gaba da shiryar da shi da kuma ba shi ikon yi wa Najeriya hidima cikin nasara..

    birthday greets pbat Shettima
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleCOMMANDANT NACOLM CHARGES STUDENTS OF LMC TO WORK IN HARMONY AND CREATE ROOM FOR INTELLECTUAL DIALOGUE ‎
    Next Article Gombe APC Gubernatorial candidate, Gwamna Recomits to Human Capital Development, Youth Mentorship.

    Related Posts

    News

    Shugaba Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin Zurmi

    September 2, 2026
    News

    Zulum greets VP Shettima @60, says low-key celebration portrays humility

    September 2, 2026
    News

    Gov. Yusuf celebrates VP Shettima at 60, hails his leadership qualities

    September 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026294 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026242 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026225 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026168 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026165 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026156 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.