Shugaban sashin Kuɗi da Mulki na Ƙaramar Hukumar Funtua, Alhaji Ibrahim Yahaya Malumfashi, ya gana da ma’aikatan ƙaramar hukumar domin bayyana musu halin da ake ciki dangane da tsarin PENCOM.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da Bashir YeroJami’in Watsa Labarai na Ƙaramar Hukumar Funtua ya samarwa manema labar
Ya ce a yayin ganawar, Alhaji Ibrahim Yahaya Malumfashi ya bayyana cewa kusan dukkan ma’aikatan da ke aiki a Ƙaramar Hukumar Funtua a halin yanzu ba su shiga cikin tsarin PENCOM ba. Ya ce, bisa bayanin da aka yi musu, ma’aikatan da za su yi ritaya daga yanzu zuwa watan Nuwamba na shekarar 2055 ba su cikin wannan tsarin na Pencom.
Saboda haka, ya yi kira ga ma’aikatan da su guji sauraron jita-jita ko yaɗa bayanan da ba su da tabbas, domin kauce wa shiga cikin ruɗani.
Haka kuma, ya shawarci ma’aikatan da kowa ya nemi wata sana’a da zai riƙa yi domin ƙara bunƙasa tattalin arzikinsa, musamman a fannoni kamar noma, kiwo da sauran sana’o’i masu amfani.
Shugaban sashin Kuɗi da Mulkin Alhaji Ibrahim Yahaya Malumfashi ya kuma miƙa godiyarsa ga shugaban hukumar da ke kula da horarwa da ɗaukar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Jihar Katsina, Alhaji Usman Mamman Maska, bisa ƙoƙarin da yake yi na horas da ma’aikata da kuma ɗora su kan tsarin aiki mai kyau domin kauce wa matsaloli yayin gudanar da ayyukansu na gwamnati.
Haka kuma, ya gode wa Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, bisa yadda gwamnatin jihar ke biyan albashi, fansho da sauran haƙƙoƙin ma’aikatan ƙananan hukumomi a kan lokaci.
A nasa jawabin, Daraktan Sashen Kula da Ma’aikata (Personnel Management Department), Alhaji Lawal Aliyu Faskari, ya bayyana cewa an kira su zuwa Katsina, inda aka yi musu cikakken bayani kan yadda tsarin PENCOM yake.
Ya ce, wannan ne ya sa aka kira taron ma’aikatan domin a bayyana musu tsarin a hukumance, tare da fayyace duk wasu bayanai da suka shafi tsarin, domin kauce wa yaɗuwar jita-jita da ruɗani.
Alhaji Lawal Aliyu Faskari ya kuma gargadi ma’aikatan da su guji yin rubuce-rubuce ko wallafa bayanai a kafafen sada zumunta ba tare da dalili ko cikakken bayani ba, domin yin hakan na iya jawo wa mutum matsala.









