Tattalin arzikin Najeriya ya ci gaba da samun bunƙasa a zango na biyu na shekarar 2026, inda GDP ɗin ƙasar ya ƙaru da kashi 4.43 cikin 100, idan aka kwatanta da kashi 4.23 a makamancin wannan lokaci na shekarar 2025 da kuma kashi 3.89 a zangon farko na 2026, a cewar Ma’aikatar Kuɗin Tarayya.
Ma’aikatar ta ce wannan ci gaban ya ɗaga matsakaicin bunƙasar tattalin arzikin ƙasar a farkon rabin shekarar 2026 zuwa kashi 4.16 cikin 100, daga kashi 3.68 da aka samu a makamancin wannan lokacin shekarar 2025. Ta ce kuma ci gaban ya fara yaɗuwa zuwa sassa daban-daban, inda sassa 27 na tattalin arzikin ƙasar suka samu bunƙasar sama da kashi uku a zangon na biyu, idan aka kwatanta da 23 a bara.
A fannin samar da kayayyaki, masana’antu sun samu bunƙasa da kashi 3.24 cikin 100, daga kashi 1.60 a zangon makamancin wannan na shekarar 2025, yayin da noma ya ƙaru da kashi 4.39 daga kashi 2.82. Haka kuma, ɓangaren ayyuka, wanda shi ne mafi girma wajen tallafa wa tattalin arzikin ƙasar, ya bunƙasa da kashi 4.60 daga kashi 3.94.
Ma’aikatar ta kuma ce ƙarin darajar naira da daidaito a kasuwar canjin kuɗi sun taimaka wajen ƙara darajar tattalin arzikin Najeriya idan aka auna shi da dalar Amurka. A cewarta, naira ta samu ƙarin daraja da sama da kashi 12 cikin 100 tsakanin farkon rabin shekarar 2025 da na 2026, lamarin da ya taimaka wajen ƙara darajar tattalin arzikin ƙasar da kusan kashi 17 cikin 100 a ma’aunin dalar Amurka.
Ma’aikatar Kuɗin ta ce wannan ci gaba na nuna cewa Najeriya na kan hanyar cimma burin Gwamnatin Tarayya na mayar da tattalin arzikin ƙasar ya kai dala tiriliyan ɗaya nan da shekarar 2030. Ta ce Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) ya sanya Najeriya cikin ƙasashe 10 da ake sa ran za su fi bayar da gudunmawa ga bunƙasar tattalin arzikin duniya a 2026, yayin da gwamnati ta jaddada buƙatar ci gaba da sauye-sauyen tattalin arziki domin tabbatar da cewa ci gaban ya koma ga talakawa da sauran ‘yanƙasa.
Sabuwar Nigeria

