A wani bangare na bada kulawa ga sha’anin tsaro a cikin wakilcin sa Danmajalisar Tarayyar mai kula da Kananan Hukumomin Bungudu/Maru Hon. Dakta Abdulmalik Zubairu Zannan Bungudu ya ziyarci sansanonan JAMI’AN SOJI dake yankunan Dansadau da Magami da kuma Daraga/Dankurmi dukkan su a cikin yankin da yake yiwa wakilci.
Wannan bayanin yana kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da Mai Magana da yawun Dan majalisar,Jakadan bungudu, Aminu Lawal bungudu ya rabawa manema labarai.
Sanarwar ta ce, Ziyarar sansanonan wadda ta gudana a kwanan nan ta biyo bayan kokarin Wakilin na karfafawa sha’anin tsaron al’ummar sa musamman a wadannan yankuna da ayukkan yan bindiga ke yiwa barazana babu dare babu rana.
A cikin jawabin sa a dukkan wuraren da ya ziyarta, Zannan Bungudu ya karfafa wa zaratan JAMI’AN SOJIN guiwa akan yadda suke kokarin kare rayukka da dukiyyoyin al’umma, yana mai cewa matsalar tsaro na daga cikin abinda wakilcin sa yake baiwa fifikon gaske.
Zannan Bungudu ya bukaci Jami’an Sojin da kada suyi kasa a guiwa wajen gudanar da aikin su tare da shaida masu cewar a shirye yake ya tallafa ga dukkan bukatocin su gwaegwadon hali a duk lokacin da aka gabatar masa.
Ya jajanta masu akan yadda ayukkan yan bindiga ke ta’adi ga Jami’an su, yana mai tabbatar masu cewa duk wanda ya rasa rayuwa a cikin wannan aiki babu shakka yana da kyakkyawan sakamo a gobe Kiyama.
Sai dai ya bukaci al’umma da su bada cikakken hadin kai ga Jami’an tsaron domin kakkabe ayukkan yan ta’addan.
Yawaitar ayukkan yan bindiga da yanayin yadda tattalin arzikin wadannan yankuna yaci karo da koma baya shine ya haifar da Wakilin ya bada umarnin cigaba da daukar nauyin dukkan al’ummar da yan bindigar suka yiwa rauni ba tare da jinkiri ko la’akari da inda suka fito ba.
Ziyartar wadannan yankuna dake fama da matsalar tsaro da Zannan Bungudu ke yi ya zame masa dabi’a tun bayan zaman sa Wakilin al’umma a shekarar 2015.
Idan za’a iya tunawa, bukata ta farko da Zannan Bungudu ya gabatarwa Majalisar tarayya a shekarar 2015 ita ce bukatar inganta tsaro a wadannan yankuna lamarin da haifar da aka aiwatar da shirin atisayen Jami’an Sojin Nijeriya na shekarar a yankin Dansadau.
Tuni dai da Wakilin ya dawo gida bayan kwashe kwanaki biyu na wannan ziyara a wadannan yankuna.
Allah SWT Ya dawo muna da zaman lafiyar mu hadi da Yalwar arziki.




