Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziƙi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya kai ziyarar gani da ido a yau Litinin, 17 ga Agusta, 2026, domin duba yadda aikin Babbar Hanyar Sokoto–Badagry ke gudana a yankin jihar Kebbi.
Sabuwar Nigeria ta ruwaito Ministan yana yabawa da ƙoƙarin ma’aikatan, tare da ƙarfafa gwiwarsu wajen ci gaba da aikin.
Hanyar na daga cikin muhimman ayyukan Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma ana sa ran kammala hanyar zai sauƙaƙa zirga-zirga tsakanin Arewa da Kudu maso Yamma, da kuma rage lokacin tafiya, da bunƙasa kasuwanci.






