A watan Mayun 2023, lokacin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta fara aiki, jihohi 27 daga cikin 36 na Najeriya na fuskantar matsalar biyan albashin ma’aikatansu, yadda ya kamata. Shekaru uku bayan haka, wannan adadi ya sauya, babu wata jiha da take kasa biyan albashin ma’aikatan ta a cewar alkaluman da gwamnatin tarayya ta gabatar a cikin “Nigeria’s Reform Scorecard”.
Wannan sauyi na zuwa ne bayan wasu manyan sauye sauyen tattalin arziki da suka hada da cire tallafin man fetur da sake fasalin tsarin canjin kudaden waje. Tsakanin Yunin 2023 da Disamban 2025, an samu Naira tiriliyan 15.8 na tanadin kudaden tallafin man fetur, inda aka raba wa jihohi da kananan hukumomi Naira tiriliyan 10.4.
Karin kudaden da jihohi suka samu ya kara musu azamar gudanar da ayyukansu, ciki har da biyan albashi da kuma daukar nauyin ayyukan ci gaba. A matakin tarayya kuma, an ware Naira tiriliyan 9.39 domin karin albashi, sabon mafi karancin albashi da alawus-alawus ga ma’aikatan gwamnati.
Wannan ya kuma taimaka wajen samun karin albarkatun da suka bai wa gwamnati damar kara mafi karancin albashi daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000. Bayanai irin wadannan na nuna cewa gyaran tattalin arziki ba ya tsaya kan alkaluman gwamnati kadai ba, yana shafi ma’aikata da iyalansu kai tsaye.
Duk da cewa har yanzu akwai kalubalen tsadar rayuwa da bukatar kara inganta jin dadin jama’a, sauyi daga jihohi 27 masu fama da matsalar albashi zuwa yanzu da babu wata jiha da ke da wannan kalubalen na daga cikin muhimman alamomin da ke nuna kokarin sake gina tsarin tattalin arzikin Najeriya. Gyaran ya fara samar da daidaito, babban aikin yanzu shi ne tabbatar da amfaninsa ya isa ga talaka.

