Gwamnatin Tarayya ta ƙara nuna himmarta wajen farfaɗo da ilimin manyan makarantu, inda Asusun Tallafawa Manyan Makarantu na Ƙasa (TETFund) ya ware kusan Naira Biliyan 2.53 ga kowace jami’ar gwamnati, Naira Biliyan 1.87 ga kowace kolejojin kimiyya da fasaha,Polytechnic, da Nairan Biliyan 2.06 ga kowace Kwalejin Ilimi a ƙarƙashin shirin tallafin shekarar 2026.
Kafar Sadarwar Sabuwar Nigeria ta ce Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a Lokoja yayin taron TETFund na shiyyar Arewa ta Tsakiya.
Mohammed Idris ya ce tallafin na nuna ƙudirin Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ƙarfafa ilimi da bunƙasa ƙwarewar matasan Najeriya. Ya ce kuɗaɗen za su taimaka wajen ginawa da gyaran ɗakunan karatu da sauran muhimman gine-gine, samar da kayan dakunan gwaje-gwaje, inganta ɗakunan karatu da kuma ƙara tallafa wa bincike da ƙirƙire-ƙirƙire. Ya jaddada cewa gwamnati na kallon ilimi a matsayin muhimmiyar hanya wajen samar da ƙwararrun matasa da za su taimaka wajen gina tattalin arzikin ƙasa.
Ministan ya kuma ce tallafin TETFund a ƙarƙashin Renewed Hope Agenda ya wuce samar da gine-gine kawai, inda ake ƙara mai da hankali kan fasahar zamani ta Artificial Intelligence, Kwarewar Yanar Gizo, bincike, ƙirƙire-ƙirƙire da horar da ma’aikatan ilimi. Ya buƙaci manyan makarantu su daidaita bincike da shirye-shiryen karatu da buƙatun tattalin arziki, musamman a fannonin noma, ma’adinai, makamashi, masana’antu da fasahar zamani. Ya ce ilimi mai inganci da ƙwarewa na taimakawa wajen rage rashin aikin yi da kuma samar da matasa masu iya taka rawa wajen ci gaban ƙasa.
A nasa jawabin, Gwamnan Kogi, Ahmed Ododo, ya yaba da ayyukan TETFund wajen bunƙasa manyan makarantu, yana mai kira da a ƙara zuba jari a bincike da ƙirƙire-ƙirƙire. Shi ma mamba a Kwamitin Amintattu na TETFund mai wakiltar Arewa ta Tsakiya, Dakta Abdulrahman Ocholi, ya ce tallafin gwamnatin Tinubu ya haɗa da robotics da coding, 3D printing, makamashi, dakunan binciken AI da biotechnology, mini-grid power projects da innovation hubs. Ya ce hakan na nuna yadda Gwamnatin Tarayya ke ƙoƙarin sauya manyan makarantu zuwa cibiyoyin samar da ilimi, ƙwarewa da sabbin hanyoyin magance matsalolin ƙasa.

