Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Babbar Hanyar Sokoto Zuwa Badagry Mai Tsawon Kilomita 1000 Za ta Bunkasa Noma a Arewa – Mohammed Idris
    News

    Babbar Hanyar Sokoto Zuwa Badagry Mai Tsawon Kilomita 1000 Za ta Bunkasa Noma a Arewa – Mohammed Idris

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 13, 20262 Mins Read
    FB IMG 1786651322205
    FB IMG 1786651322205

     

    Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce aikin babbar hanyar da za ta tashi daga Sokoto zuwa Badagry jihar Lagos,mai tsawon kilomita 1,000 za ta taimaka wajen bunƙasa noma da buɗe sabbin damar tattalin arziki ga al’ummomi da jihohin da hanyar za ta ratsa, ciki har da Jihar Kebbi.

    Idris ya bayyana haka ne a Abuja, lokacin da Ayarin masu yaɗa labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Yakubu Birnin-Kebbi, suka kai masa ziyarar ban girma. Ya ce kusan kilomita 250 daga cikin hanyar za su ratsa jihar Kebbi, lamarin da zai bai wa jihar damar ƙara faɗaɗa harkokin noma, kasuwanci da sauran ayyukan tattalin arziki.

    Ministan ya ce aikin ba wai hanya ce kawai ta haɗa garuruwa da jihohi ba, domin ana sa ran samar da madatsun ruwa kusan 63 a kan layin hanyar, waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa noma, samar da lantarki da sauran ayyukan tattalin arziki. Ya kuma yaba wa Gwamnatin Kebbi kan haɗin gwiwar da take yi da Gwamnatin Tarayya a fannonin noma, ababen more rayuwa da tsaro.

    Alh Mohammed Idris ya ce irin waɗannan manyan ayyukan more rayuwa na daga cikin ƙoƙarin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ke yi don janyo gwabnati kusa da jama’a, tare da samar da kyakyawan yanayin da zai bai wa ‘yan kasuwa da al’umma damar bunƙasa. A cewarsa, yawancin al’ummar Najeriya suna zaune ne a jihohi, ba Abuja ba, don haka ya zama wajibi a kai ci gaba inda jama’a suke.

    A nasa jawabin, Kwamishinan Yaɗa Labarai na Kebbi ya ce Ayarin sun je Abuja ne domin gabatar wa ministan bayanai kan nasarorin da gwamnatin jihar ta samu tare da ƙarfafa alaƙarta da Gwamnatin Tarayya. Ya ce Kebbi na da babbar dama a fannonin noma, ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da tsaro, kuma jihar na ƙudurin ci gaba da haɗa hannu da Gwamnatin Tarayya domin amfani da wannan damar wajen bunƙasa tattalin arziƙin jihar.

    FB IMG 1786651326222
    FB IMG 1786651326222
    FB IMG 1786651313902
    FB IMG 1786651313902
    FB IMG 1786651308647
    FB IMG 1786651308647
    FB IMG 1786651301676
    FB IMG 1786651301676
    alherinta badagry hanyar Idris minista sokoto
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleA Shirye shiryen Aikin Hajji mai zuwa: Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kamfanonin Jirage Sama Biyar Don Jigilar maniyata aikin Hajjin 2027
    Next Article KANO STATE PILGRIMS WELFARE BOARD REDUCES HAJJ DEPOSIT, MAINTAINS REGISTRATION DEADLINE

    Related Posts

    News

    Kebbi Governor Donates N50m Empower Persons with Special Needs

    August 13, 2026
    News

    POLICE FOIL BANDITS’ ATTACK IN ZURMI, RENDER SUSPECTED IED SAFE IN BUKKUYUM

    August 13, 2026
    News

    LISTENERS OF FRCN KADUNA WANTS THE FEDERAL GOVERNMENT TO TAKE URGENT STEPS TO BRING BACK THE STATION ON AIR

    August 13, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026283 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026239 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026218 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026164 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026157 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026151 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.