Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Hukumar Aikin Hajji ta kasa,NAHCON ta Sanar Da Kudin kujerar Hajjin 2027, Ta Kayyade Ranar Ƙarshe Ta Biyan Kuɗin Maniyyata
    News

    Hukumar Aikin Hajji ta kasa,NAHCON ta Sanar Da Kudin kujerar Hajjin 2027, Ta Kayyade Ranar Ƙarshe Ta Biyan Kuɗin Maniyyata

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 15, 20262 Mins Read
    FB IMG 1786781774198
    FB IMG 1786781774198

    Daga Aliyu Samba

    Hukumar Aikin Hajji i ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2027 da Gwamnatin Tarayya ta amince da su, tare da kayyade wa jihohi ranar 2 ga watan Disamba 2026 a matsayin ranar ƙarshe ta tura dukkan kudaden Hajjin.

    Hukumar ta ce an ƙayyade kudaden ne bayan tuntubar shugabannin Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi da masu samar da ayyukan Hajji a Ƙasar Saudiyya, tare da la’akari da farashin musayar kuɗi da kuma tsadar ayyukan da ake samarwa.

    NAHCON ta bayyana cewa kudin kujerar Hajjin ya bambanta bisa yankin da alhazai za su tashi, inda alhazan yankin Maiduguri da Yola za su biya N7,560,822, yayin da na sauran jihohin yankin Arewa za su biya N7,672,822.

    Alhazan yankin Kudanci kuwa za su biya N7,882,822 a matsayin kudin aikin Hajjin 2027.

    Hukumar ta ce maniyyatan da suka riga suka ajiye N5,000,000 za su kammala biyan ragowar kudin domin kammala rajistarsu, yayin da sabbin maniyyata za su biya kudin ne ta hannun Hukumomin Jin Daɗin Alhazai, hukumomi ko kwamitocin jihohinsu, ko kuma bankunan da ke cikin tsarin adashin Aikin Hajji,wato Hajj Savings Scheme (HSS).

    NAHCON ta kuma kayyade ranar 26 ga watan Satumba 2026 a matsayin ranar ƙarshe da za a kammala shigar da bayanan kimiyyar halittu (biometric data) na dukkan maniyyatan Hajjin 2027 a tsarin dijital na Nusuk-Masar.

    Hukumar ta jaddada cewa babu wani ƙarin lokaci da za a bayar bayan wannan wa’adi, saboda tsarin daidaita bayanan maniyyata da rabon kujerun jiragen sama ya dogara ne da kammala biyan kudade da shigar da bayanai cikin lokaci.

    NAHCON ta yi gargadin cewa rashin cika waɗannan wa’adodi na iya haifar da rasa kujerar Hajjin da aka ware wa maniyyata ko jihohin da abin ya shafa.

    Hukumar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na tabbatar da gaskiya, rage tsadar gudanar da aikin Hajji da kuma kare walwalar alhazan Najeriya yayin shirye-shiryen aikin Hajjin 2027.

    Sabuwar Nigeria.

    hajji kudin kujerar nigeria
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleProf. Bunkure Urges Universities to Adapt to Emerging Digital Technologies
    Next Article Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar NPERA Ta 2026

    Related Posts

    News

    Governor Abba Kabir Yusuf Emphasizes Importance of Orange Economy in Creating Jobs and Driving Economic Growth

    August 16, 2026
    News

    PRESIDENT TINUBU: ADELEKE’S VICTORY, A FITTING ASSURANCE THAT DEMOCRACY WILL CONTINUE TO FLOURISH IN OUR COUNTRY

    August 16, 2026
    News

    SPEAKER ABBAS EMPOWERMENT : ANOTHER BATCH EMPOWERED IN VARIOUS EMPOWERMENT SCHEME.

    August 16, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026283 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026240 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026220 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026164 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026157 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026151 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.