Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote Dake Wudil Ta Karɓi Naira Miliyan 180.3 na Lamunin Karatu Ga Dalibai 2,152 daga NELFUND
    Education

    Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote Dake Wudil Ta Karɓi Naira Miliyan 180.3 na Lamunin Karatu Ga Dalibai 2,152 daga NELFUND

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 17, 20262 Mins Read
    FB IMG 1786983927542
    FB IMG 1786983927542

    Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya bai wa dalibai 2,152 na Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote (ADUSTECH), Wudil, Jihar Kano, tallafin lamunin karatu na Naira miliyan 180.3 domin zangon karatu na 2025/2026.

    Wata wasika da jami’ar ta aikewa NELFUND mai dauke da kwanan wata 13 ga Yuli, 2026, ta tabbatar da cewa kudaden sun shiga asusun jami’ar domin biyan kudin daliban da suka ci gajiyar shirin.

    Takardar ta bayyana cewa an biya kudaden ne a rukuni hudu, inda rukunin K ya samu Naira miliyan 78.9 ga dalibai 946, yayin da rukunin L ya samu Naira miliyan 75.8 ga dalibai 900.

    Haka kuma, rukunin M ya samu Naira miliyan 20.6 ga dalibai 247, yayin da rukunin N ya samu Naira miliyan 4.9 ga dalibai 59.

    Jimillar kudaden da jami’ar ta karba ya kai Naira miliyan 180,346,256, wadanda suka shafi dalibai 2,152 a zangon karatun 2025/2026.

    Jami’ar ta bayyana godiyarta ga NELFUND bisa shigar da dalibanta cikin shirin lamunin karatu, tana mai cewa tallafin zai taimaka wajen rage musu nauyin kudaden karatu da sauran bukatun ilimi.

    Kafar Sadarwar Sabuwar Nigeria ta ce Shirin lamunin karatu na NELFUND na daga cikin matakan da gwamnatin Tarayya ke amfani da su wajen rage matsalolin kudi da ke hana wasu dalibai ci gaba da karatun jami’a da sauran manyan makarantun kasar.

    dangote nelfund univ wudil
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleGovernor Radda Backs KP3A Statewide Tour, Vows Lasting Legacy for Future Generations
    Next Article CHAIRMAN ZARIA LOCAL GOVERNMENT MOURNS MACCIDO MOHAMMED FORMER DEPUTY SPEAKER.

    Related Posts

    Education

    ASUU-KASU Raises Alarm Over Exodus of Professors, Lecturers, Issues Strike Ultimatum

    August 17, 2026
    Education

    ABU donates 45 refurbished microscopes to 8 secondary schools in Zaria

    August 15, 2026
    Education

    Prof. Bunkure Urges Universities to Adapt to Emerging Digital Technologies

    August 15, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026283 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026240 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026220 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026164 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026158 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026152 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.