Shugaba Bola Ahmed Tinubu, zai shiga cikin Jerin shugabannin kasashen duniya wajen gabatar da jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 81 (UNGA 81) a birnin New York, Amurka, ranar Laraba, 23 ga Satumba, 2026.
Kafar Sadarwar Sabuwar Nigeria,ta ce an tsara Tinubu zai kasance mai magana na 10 a zaman safiyar rana ta biyu, inda ake sa ran zai yi jawabinsa tsakanin karfe 11:30 na safe zuwa 12:00 na rana agogon New York, wato tsakanin karfe 4:30 zuwa 5:00 na yamma agogon Najeriya. Sama da shugabannin kasashe 193 ne ake sa ran Za su halarci wannan babban Taron.
Taron Na bana, wanda za a gudanar daga 22 zuwa 28 ga Satumba, zai mayar da hankali kan taken “Restoring trust, managing transformation: A United Nations that delivers for all”, wato dawo da Aminci,da kula da sauye sauye,a tsarin majalisar dinkin duniya ta kowa da kowa.
Ana kuma sa ran Tinubu zai halarci tarurruka da dama da suka shafi sauyin yanayi, hauhawar ruwan teku da shirin tunkarar annobar cututtuka, tare da ganawa da babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya mai barin gado, António Guterres.
Babban Jakadan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya, Jimoh Ibrahim, ya tabbatar da halartar Tinubu, yana mai cewa shugaban zai yi amfani da taron wajen bayyana sauye-sauyen da gwamnatinsa ke aiwatarwa tare da neman hadin kan kasashen duniya kan tsaron iyakokin Afirka ta Yamma. Ya kuma bayyana yiwuwar ganawar Tinubu da shugaban Amurka, Donald Trump, a gefen taron. Ana sa ran zaman muhawarar babban taron zai gudana daga 22 zuwa 28 ga Satumba, yayin da taron Majalisar Dinkin Duniya na 81 zai bude a hukumance tun daga 8 ga Satumba.

