Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    KADA TIMESKADA TIMES
    • Home
    • News
    • Energy
    • Entertainment
    • Health
    • Politics
    • Religion
    • Sports
    • More
      • Business
      • Education
      • Environment
      • Opinion
      • Security
      • Traditional/tourism
    Subscribe
    KADA TIMESKADA TIMES
    Home » Ba za a cimma burin samun tattalin arzikin dala tiriliyan daya ba ,sai an sa mata cikin tsare tsaren — Shettima
    News

    Ba za a cimma burin samun tattalin arzikin dala tiriliyan daya ba ,sai an sa mata cikin tsare tsaren — Shettima

    Malam Mujitaba RamalanBy Malam Mujitaba RamalanAugust 19, 20262 Mins Read
    FB IMG 1787169335073
    FB IMG 1787169335073

    Mataimakin Shugaban Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya ce burin gwamnatin tarayya na gina tattalin arzikin Najeriya mai darajar dala tiriliyan daya ba zai tabbata ba matukar ba a bai wa mata cikakkiyar dama su taka rawa a harkokin tattalin arzikin kasar ba.

    Kafar Sadarwar Sabuwar Nigeria ta ce Shettima ya bayyana haka ne ranar Laraba a Abuja, yayin taron kasa na biyu kan hada mata da harkokin tattalin arziki, #SheIsIncluded 2026, inda ya ce gwamnati ta kaddamar da wasu tsare-tsare guda hudu domin rage gibin da ke tsakanin maza da mata wajen samun damar harkokin kudi. Ya ce kashi 47 cikin 100 na matan Najeriya ne ke da asusun kudi na zamani, idan aka kwatanta da kashi 58 cikin 100 na maza.

    Ya ce gwamnati ta mayar da hankali wajen hada mata da matasa da ilimi, jari, kasuwanni da sabbin damammakin tattalin arziki, tare da jaddada cewa zuba jari a mata ba taimako na jin kai ba ne, dabarar bunkasa tattalin arziki ce. A nata bangaren, Ministar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta ce burin dala tiriliyan daya ba zai cika ba idan ba a shigar da mata, musamman wadanda ke aiki a bangaren tattalin arzikin karkara da na yau da kullum, cikin shirin sauyin tattalin arzikin kasar ba.

    Ministar ta kuma bayyana cewa shirin Nigeria for Women Programme Scale-Up ya fadada tsarin kungiyoyin mata zuwa mata miliyan 4.5 da aka tsara cikin kungiyoyi 300,000 a fadin Najeriya. Ta ce a matakin farko, an hada mata sama da 560,000 cikin kungiyoyi fiye da 26,000, inda suka tara sama da Naira biliyan 4.9 daga albarkatun kansu tare da samun tallafin rayuwa na kusan Naira biliyan 15.6. Haka kuma, gwamnati ta bayyana wasu tsare-tsare hudu da suka hada da samar da tsarin amintaccen amfani da fasahar zamani, amfani da bayanai wajen tabbatar da gaskiya, hadin gwiwar samar da kudade da National Income Activation Initiative domin mayar da hada mata da harkokin kudi zuwa samar da kudin shiga da ayyukan yi..

    FB IMG 1787169330270
    FB IMG 1787169330270
    FB IMG 1787169323554
    FB IMG 1787169323554
    FB IMG 1787169318393
    FB IMG 1787169318393
    FB IMG 1787169313381
    FB IMG 1787169313381
    activities economic in role women
    Share. Facebook Twitter WhatsApp LinkedIn Email Telegram Copy Link
    Previous ArticleTaimakawa Dalibai: Shugaba Tinubu ya ba da umurnin a mayar da kuɗaɗen da EFCC ta kwato zuwa hukumar ba da tallafin karatun Dalibai,NELFUND
    Next Article Tinubu ya ba da umurnin a tsara sabbin dabarun tabbatar da shirin tsaron Najeriya na

    Related Posts

    News

    FEDERAL GOVERNMENT FLAGS OFF 250-UNIT RENEWED HOPE CIVIL SERVICE ESTATE IN GWAGWALADA.

    August 19, 2026
    News

    Governor Radda Flags Off 90,000 Bags of Grains to Vulnerable Households in Katsina, Orders Fair Distribution

    August 19, 2026
    News

    Chairman Lake Chad Basin Governors’ Forum Gov. Mai Mala Buni Visits Nigerian Refugees in Kaya, Chad.

    August 19, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Governor Radda Extols Tinubu as Four Katsina Sons Clinch Federal Appointments

    April 2, 2026285 Views

    Retired Police Officers Plan “Do-or-Die” Peaceful Protest at Villa April 20

    April 5, 2026240 Views

    Emir of Katsina Approves Turbanning of Three Illustrious Sons

    April 1, 2026220 Views

    Saulawa Assumes Office as Acting Customs Provost Marshal, Promises Fair Enforcement of Discipline

    April 25, 2026164 Views

    GENERAL BABANGIDA APPLAUDS AFCSC INITIATIVE, URGES DEEPER COMMUNITY ENGAGEMENT FOR SECURITY

    May 12, 2026158 Views

    FORMER CHAIRMAN MHWUN KATSINA STATE, COMRADE MANNIR, APPEALED TO THE STATE GOVERNMENT TO FULFILLED PROMISE OF PAYING RETIRED WORKERS IN LOCAL GOVERNMENTS.

    May 12, 2026154 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    © 2026 Kada Times. | Developed by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About Us
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Contact Us

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.